Labarai
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar rigakafi tare da raba jaka da sauran kayayyaki ga maniyyatan aikin Hajjin 2024.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga wakilin gidan rediyon Najeriya a hedikwatar hukumar da ke Dutse, babban birnin jihar.
Ya yi bayanin cewa allurar rigakafin ga dukkan maniyyatan jihar na daga cikin sharuddan hukumar Saudiyya na bayar da biza.
A cewarsa, ana sa ran za a fara allurar rigakafi da rarraba kayayyakin a cibiyoyin bitar Alhazai da ke fadin kananan hukumomin jihar ashirin da bakwai.
Ya kara da cewa, ana ci gaba da gudanar da taron bita ga Maniyyata a dukkan cibiyoyin da aka kebe a fadin jihar.
Ya ce, hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta kammala dukkan shirye-shiryen jigilar Alhazan jihar zuwa kasa mai tsarki cikin sauki.
Ya kuma bayyana cewa hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ce ta tsara jigilar maniyyatan jihar ta bana, inda ta bai wa kamfanin Max Air damar jigilar Maniyyatan jihar zuwa kasar Saudiyya.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar