Labarai
An Kama Matasa Uku Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Rundunar ƴan sanda a jihar Nasarawa ta cafke wasu matasa uku kan zarginsu da haɗa baki don yunƙurin yin garkuwa da kawun ɗaya daga cikinsu.
Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Rahman Nansel ya sanyawa hannu, waɗanda ake zargi sun yi barazanar sace mutumin idan ya ƙi biyansu kuɗin fansa.
Sanarwar ta ce fargabar kada a sace shi ta sa mutumin ya tanadi kuɗin da matasan suka buƙaci ya ba su, inda ya ajiye shi a wurin da suka nema daga nan kuma suka kwashi kuɗin tare da rabawa a tsakaninsu.
Waɗanda ake zargin sun amsa laifin da ake zarginsu da yi sannan sanarwar ta ce ana ƙoƙarin bankaɗo wanda ya tsere.
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar