Labarai
Jiragen Soji Sun Kashe Kwamandojin ISWAP A Borno
Farmakin Rundunar Sojin Saman Najeriya a maboyar ‘yan ta’addar ISWAP ya hallaka sama da kwamandojin ‘yan bindiga 30 a kauyen Kolleram da ke gabar tafkin Chadi, a Jihar Borno.
Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojojin saman Najeriya, AVM Edward Gabkwet, ya sanar cewa daga cikin manyan kwamandojin ’yan ta’addan da aka kashe a harin akwai Ali Dawud da Bakura Fallujah da kuma Malam Ari.
Sanarwar da Gabkwet, ya fitar ranar Talata a Abuja ta ce jiragen yakin Operation Hadarin Kai na Sojin Saman Najeriya sun kai farmakin ne ranar Asabar 13 ga Afrilu.
Ya bayyana cewa, harin ya yi wa ’yan ta’addanci mummunan illa a yankin Arewa maso Gabas, wanda hakan wata garumar nasara ce ga yunkurin dakile ta’addanci a yankin.
“Bugu da kari, harin ya lalata motocin ’yan ta’adda da dama da babura, da kayayyakin amfaninsu, wanda hakan cikas ne ga ayyukan ‘yan ta’addan.
“Bayanan sirrin da aka tattara bayan harin saman sun nuna cewa bama-bamai da aka harba sun lalata wata cibiyar ’yan ta’adda da ke cikin yankin Kolleram, inda suke sarrafa abinci da sauran abubuwa.
“Nasarar wadannan hare-hare ta sama na kara jaddada kudurin Rundunar Sojin Najeriya na kawar da ta’addanci da kuma tabbatar da tsaron ’yan kasa.
“Aikin ya yi matukar nasarar rage karfin kungiyar ISWAP a yankin ta hanyar kawar da manyan ’yan ta’adda da lalata kayayyakin aikinsu.”
PR/Usman Sani./Wababe
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana