Connect with us

Kasuwanci

Gwamnan Jigawa Namadi Na Jagorantar Ziyarar Nazarin Noman Alkama a Habasha

Published

on

 

Gwamnan jihar Umar Namadi ya fara wani gagarumin ziyarar gani da ido zuwa kasar Habasha tare da wata babbar tawaga da ta hada da manyan mataimaka a harkokin noma, jami’ai, da kwararru daga ma’aikatar noma ta jihar da hukumomin da abin ya shafa.

 

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na gwamnan Hamisu Mohammed Gumel ya raba wa gidan rediyon Najeriya ya bayyana cewa, makasudin ziyarar shi ne nazarin shirin noman alkama na kasar Habasha da kuma gudanar da wani cikakken shiri da manufar dawowa gida sabbin dabaru da kwarewa zuwa gida

 

A cewarsa, alkama, kasancewarta ta biyu mafi girman abin bukata a duniya, tana da matukar muhimmanci wajen magance kalubalen samar da abinci a duniya.

 

Ya ce, a bisa wannan yanayin, Habasha ta zama babbar jigo a fannin noman alkama a Afirka, wanda ya nuna gagarumar nasarar da aka samu wajen dorewar noma da samar da albarkatu.

 

Hamisu Mohammed Gumel ya ci gaba da bayyana cewa, ziyarar na da manufar cimma muhimman manufofi da suka hada da tantance shirin noman alkama na kasar Habasha da kuma fa’idarsa.

 

Ya yi nuni da cewa, sauran muradun sun hada da samar da hanyoyin yin musanyar ilimi kan tsarin noman alkama, da magance kalubalen da ake fuskanta wajen samar da alkama mai dorewa, da inganta hadin gwiwa tsakanin Habasha da Najeriya wajen daukar sabbin dabarun noma.

 

Ya bayyana cewa musamman wuraren da aka fi mayar da hankali a kai sun hada da fahimtar tsare-tsare na dogon lokaci na Habasha na noman alkama, da tantance ci gaban da aka samu da kalubale, da binciko hanyoyin samar da kayayyaki daban-daban, da kuma baje kolin ingantattun samfura kamar noma kasuwanci.

 

Ya ce, a ziyarar aiki ta kwanaki hudu, tawagar ta Jigawa, da wasu muhimman abubuwa, za su dauki darussa kan noman ruwan sama da noman alkama na ban ruwa a jihohi daban-daban na kasar Habasha, da kuma samun nasarar samar da alkama mai dorewa.

 

Hakama yayi nuni da cewa, jihar Jigawa a halin yanzu ita ce kan gaba wajen noman alkama a Najeriya, wanda ke bayar da gudunmawa sosai a fannin noma da samar da abinci, kuma ana sa ran rangadin binciken zai bude wa jihar damammaki tare da cimma wasu muhimman sakamako da za su taimaka wajen bunkasa noman alkama mai dorewa a jihar.

 

Gumel ya kara da cewa, ziyarar ta jaddada kudirin gwamnatin Gwamna Umar Namadi a jihar na binciko sabbin hanyoyin noma domin inganta samar da abinci da kuma mayar da harkar noma sana’ar kasuwanci ga al’ummar jihar da galibin masu noma ne.

USMAN MZ?Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai13 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai14 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai15 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi16 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai1 day ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara