Connect with us

Labarai

Kachalla Ɗan Ƙarami Ya Kashe Abokin Gabarsa A Zamfara

Published

on

Kasurgumin dan ta’addar da ya addabi yankin Batsari a Jihar Katsina da wani yanki na Jihar Zamfara  ya gamu da ajalinsa a hannun Kachalla Dan Karami.

Wata majiya mai tushe daga Batsari a Jihar Katsina ta tabbatar mana da cewa Kachalla Dan Karami ya fille kan Dangote ne a wani mummunan faɗa da aka gwabza a Dunmurun da ke Karamar Hukumar Zurmi a Zamfara.

Kachalla Dankarami ya yi sanadiyar kashe Dangote ne tare da wasu kannensa guda biyu da ke addabar Jihar Katsina da wani yanki na Jihar Zamfara a safiyar ranar Lahadi da ta gabata.

Rahotanni sun tabbatar da cewa Dan Karami da tawagarsa sun yi wa Dangote da yaransa kwanton ɓauna ne a daren Asabar, inda suka fara gwabzawa har safiyar ranar Lahadin da ta gabata.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta bayyana mana cewa tun da farko dai yaran Dangote ne suka kashe yaron Kachalla Dan Karami sakamakon sace musu tumaki da aka yi.

“Abin da ya faru shi ne, ɗaya daga cikin yaran Dan Karami ya saci garken tumakin ɗaya daga cikin ’yan uwan Dangote, Sale Lamo, sai yaran Dangote suka bi sawun tumakin suka karɓo su, sannan suka kashe yaron.”

“A lokacin da abin ya faru Dan Karami yana wani gari da ake kira Rukudawa, sai aka ba shi labarin abin da ya faru, kuma ya yi azama ya taho domin ɗaukar fansa.

“Da  ya isa Dumburum, sai ya ji an ce Dangote ya yi shiri zai zo ya yaƙe shi, daga nan ne ya yanke shawara, ya yi musu kwanton ɓauna,  ya samu sa’ar kashe Dangote da yaransa Lamo na Balewa da Usman Yalo.”

Labarai

Labarai22 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai23 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai24 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi1 day ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara