Connect with us

Ilimi

Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da fitar da Naira Biliyan 3 a matsayin  tallafin hadin gwiwa na kowace shekara  domin inganta ilimi a matakin farko, wato UBEC 2025 Matching Grant.

A wata sanarwa da Kwamishinan  Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na Jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya fitar ya bayyana cewa za a yi amfani da kudaden ne wajen gina sabbin azuzuwa, gyare-gyare, haka rijiyoyin burtsatse da kuma samar da kayan koyo da koyarwa ga dalibai da malamai.

Ya ce, majalisar ta kuma amince da sama da Naira Miliyan 289 domin gina sabbin ofisoshin gudanarwa da gyare-gyare a kananan hukumomi 9 na jihar.

A cewarsa, za a yi amfani da kudaden ne wajen gina ofisoshin gudanarwa a GDASS Imam Hassan Kafin Hausa, gina rukuni 8 na wuraren ba-haya a wasu makarantun IEB da aka zaɓa, da kuma ayyukan gyare-gyare a GGASS Danzomo da SAIS Hadejia.

Ya ce waɗannan matakai na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen inganta ilimi da habaka ƙwarewar ɗan adam.

Sagir Musa Ahmed ya bayyana cewa makarantun da za a yi wa ayyukan sun haɗa da GDASS Imam Hassan a Karamar Hukumar Kafin Hausa, GDASS Danzomo a Karamar Hukumar Sule Tankarkar, SSIS Hadejia a Karamar Hukumar Hadejia, da GDASS Tarubu a Karamar Hukumar Kirikasamma.

Sauran sun haɗa da GDASS Sani Ayu a Karamar Hukumar Gumel, GDASS Shuarin a Karamar Hukumar Kiyawa,
GDASS Kaugama a Karamar Hukumar Kaugama, GDASS Kwaimawa a Karamar Hukumar Dutse, da GDASS Harbo Tsohuwa a Karamar Hukumar Miga.

Kwamishinan ya ƙara da cewa majalisar ta kuma amince da kwangilar sama da Naira Biliyan 1 domin gyaran tsofaffin gine-ginen cibiyoyin kiwon lafiya 30 da aka farfaɗo da su a bara.

Game da batun haɗin gwiwa don rage talauci kuwa, Sagir ya bayyana cewa majalisar ta amince da kashe Baira Miliyan 600 domin sabunta da faɗaɗa rajistar jin daɗin jama’a ta jihar ga Hukumar Jigawa Operation Coordination Unit da Hukumar CARES ta jihar (SCCU), kasancewar hakan shi ne sharadin shiga shirin Bankin Duniya na tallafin jin daɗin jama’a da rage talauci a jihohi.

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara