Ilimi
Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da fitar da Naira Biliyan 3 a matsayin tallafin hadin gwiwa na kowace shekara domin inganta ilimi a matakin farko, wato UBEC 2025 Matching Grant.
A wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na Jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya fitar ya bayyana cewa za a yi amfani da kudaden ne wajen gina sabbin azuzuwa, gyare-gyare, haka rijiyoyin burtsatse da kuma samar da kayan koyo da koyarwa ga dalibai da malamai.
Ya ce, majalisar ta kuma amince da sama da Naira Miliyan 289 domin gina sabbin ofisoshin gudanarwa da gyare-gyare a kananan hukumomi 9 na jihar.
A cewarsa, za a yi amfani da kudaden ne wajen gina ofisoshin gudanarwa a GDASS Imam Hassan Kafin Hausa, gina rukuni 8 na wuraren ba-haya a wasu makarantun IEB da aka zaɓa, da kuma ayyukan gyare-gyare a GGASS Danzomo da SAIS Hadejia.
Ya ce waɗannan matakai na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen inganta ilimi da habaka ƙwarewar ɗan adam.

Sagir Musa Ahmed ya bayyana cewa makarantun da za a yi wa ayyukan sun haɗa da GDASS Imam Hassan a Karamar Hukumar Kafin Hausa, GDASS Danzomo a Karamar Hukumar Sule Tankarkar, SSIS Hadejia a Karamar Hukumar Hadejia, da GDASS Tarubu a Karamar Hukumar Kirikasamma.
Sauran sun haɗa da GDASS Sani Ayu a Karamar Hukumar Gumel, GDASS Shuarin a Karamar Hukumar Kiyawa,
GDASS Kaugama a Karamar Hukumar Kaugama, GDASS Kwaimawa a Karamar Hukumar Dutse, da GDASS Harbo Tsohuwa a Karamar Hukumar Miga.
Kwamishinan ya ƙara da cewa majalisar ta kuma amince da kwangilar sama da Naira Biliyan 1 domin gyaran tsofaffin gine-ginen cibiyoyin kiwon lafiya 30 da aka farfaɗo da su a bara.
Game da batun haɗin gwiwa don rage talauci kuwa, Sagir ya bayyana cewa majalisar ta amince da kashe Baira Miliyan 600 domin sabunta da faɗaɗa rajistar jin daɗin jama’a ta jihar ga Hukumar Jigawa Operation Coordination Unit da Hukumar CARES ta jihar (SCCU), kasancewar hakan shi ne sharadin shiga shirin Bankin Duniya na tallafin jin daɗin jama’a da rage talauci a jihohi.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
