Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta gudanar da bikin bude tayin bada kwangilar samar da wutar lantarki a wasu garuruwa dake kananan hukumomin Jihar.

A lokacin da yake jawabi a yayin gudanar da bikin daya gudana a sakatariyar Jihar dake Dutse, Shugaban hukumar samar da wutar lantarki a yankunan karkara ta jihar Jigawa, Injiniya Zubairu Musa ya bayyana cewar tayin bada kwangilar samar da wutar da gyara da fadadawa gami da kammala wasu ayyukan za a yi sune a garuruwa 17.

Kazalika, Injiniya Zubairu Musa, yace wannan na daga cikin kudirori 12 na Gwamna Umar Namadi na hada wutar lantarki a kanana da matsakaitan garuruwan jihar da basu da wuta.

A cewar sa, garuruwan da za’a samar da wutar lantarkin a Dutse sun hada da Sabuwar Takur da sabuwar hanyar rukunin gidajen gwamnati na Godiya Miyetti da rukunin gidaje na Bulori da kuma makaranta ta musamman ta Mega.

Shugaban hukumar wanda ya samu wakilcin Sakataren hukumar, Barrista Auwalu Yakubu, yace sauran su ne garin Wurno a karamar hukumar Birnin Kudu da samar da wutar lantarkin a sabbin rukunin gidajen gwamnati na Birnin Kudu da Dutse da Ringim da Babura tare da Kazaure da kuma Gumel.

Sai samar da wutar lantarkin a garin Tsamiyar kwance a karamar hukumar Babura da samar da wutar lantarki a hanyar Nguru da Biranen Hadejia da Kafin Hausa a kananan hukumomin Hadejia da Kafin Hausa.

Ya kara da cewar sai gyara wutar lantarki a garuruwan Addani da Ruruma da Ringim a karamar hukumar Yankwashi da kammala aikin samar da wutar lantarki a garuruwan Tage, Siga, Garin-Wakili, Fandum, Gauta, Ona, Baturiya da Barma-Guwa a karamar hukumar Kirikasamma.

Injiniya Zubairu yace sai kuma samar da wutar lantarki a garin Gwari a Miga da kuma garin Agura a karamar Kafin Hausa.

Sauran sun hada da kammala aikin samar da wutar lantarki a Dandidi a Gagarawa da Matsa a karamar hukumar Malam-Madori da kuma aikin fadada samar da wutar lantarki a Jami’ar Khadija dake garin Majia a karamar hukumar Taura.

A nasa jawabin, wakilin hukumar tantance ayyukan kwangila ta jihar Jigawa, ya ja hankalin ‘yan kwangilar da suka nuna sha’awarsu ta gudanar da aikin da su gudanar da aiki mai inganci, tare da bin dokoki da ka’idojin gudanar da ayyukan kwangila na hukumar.

 

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara