Connect with us

Kasuwanci

‘Yan Sanda Zasu Tabbatar Da Tsaro A Lokacin Bukukuwan Sallah A Kano

Published

on

 

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ba da tabbacin a shirye ta ke na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa kafin, lokacin da bayan bukukuwan Sallah karama da za a fara gobe laraba.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Mohammad Hussein Gumel ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron masu ruwa da tsaki da sarakunan gargajiya, malamai da sauran masu ruwa da tsaki da suka shafi tabbatar da tsaro.

 

Ya ce dukkan hukumomin tsaro za su kasance cikin shiri a kowane lungu da sako da niyyar tabbatar da gudanar da bukukuwan Sallah lamui lafiya.

 

CP Mohammad Hussein Gumel ya lura cewa rundunar ta riga ta tattara dukkan rahotannin sirrin tsaro da ake bukata, don haka akwai bukatar a aiwatar da tsarin da zai tabbatar da zaman lafiya.

 

Ya yi kira ga sarakunan gargajiya da malamai da su hada kai da jami’an tsaro, yana mai jaddada cewa jihar Kano ta samu zaman lafiya sakamakon hadin kai da ke tsakanin jama’a da jami’an tsaro.

 

“Mun tsara dabarun inganta tsaro, kuma muna da kwarin gwiwar cewa shawarwarin za su yi aiki yadda ya kamata wajen ganin mun shaida bukukuwan Sallah lafiya kalau.”

 

A jawabansu daban daban wakilan sarakunan Bichi da Gaya Alhaji Nura Ahmed madakin Bichi da Alhaji Bashir Albasu, makaman Gaya sun yaba da kokarin da kuma jajircewar rundunar ‘yan sandan Kano na ci gaba da aiki babu kama hannun yaro wajen dakile ayyukan miyagun ayyuka a jihar.

 

“Wannan taron ya dace da lokacin da ya dace, saboda batun tsaro alhakin kowa ne, don haka akwai bukatar mu hada kai don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a cewar wakilan sarakunan da suka halarci taron.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

Labarai

Labarai12 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai13 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai14 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi15 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai1 day ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai2 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai2 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara