Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Da UNICEF Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Shirin Kare Hakkin Yara

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa da Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF sun rattaba hannu kan shirin aiki na shekaru 3 (2025-2027) da nufin inganta kare hakkin yara da mata, tare da tabbatar da rayuwarsu da ci gabansu a cikin jihar.

Taron sanya hannun, wanda aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Dutse, ya samu halartar Gwamna Malam Umar Namadi da kuma Shugaban Ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, tare da wasu manyan baki.

 

A jawabin sa, Gwamna Umar Namadi ya jaddada kyakkyawar alakar da ke tsakanin Jigawa da UNICEF tun daga kafuwar jihar a shekarar 1991.

Kamar yadda na saba fada, UNICEF ita ce tsohuwar abokiyar cigaban jihar Jigawa, wacce ke ci gaba da tallafa wa jihar tun bayan kafuwarta a 1991” in ji Gwamna Namadi.

Malam Umar Namadi ya gode wa UNICEF bisa jajircewarsa wajen samar da kudade da aiwatar da shirye-shirye da suka haifar da ci gaba a fannoni daban-daban.

Yayin da muke sanya hannu kan wannan shirin na shekaru uku, ina so in sake tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa za ta aiwatar da shi gaba daya, tare da yakinin cewa tare da hadin gwiwarmu za mu cimma burin da aka sanya a gaba.”

Ya jaddada cewa kowane yaro a Jihar Jigawa yana da damar samun kariya, tsira da rayuwa, bunkasa, samun ilimi, da kuma cika  burinsa a cikin iyali mai karfin tattalin arziki da kuma kyakkyawan yanayi.

Ya kara da cewa jihar za ta samar da dukkanin yanayin da ake bukata domin aiwatar da shirin, ciki har da sabunta dokoki, samar da kudade, da inganta hanyoyin hadin gwiwa domin tabbatar da ingancin shirin.

A nasa jawabin, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah ya jinjinawa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa jajircewarta wajen inganta rayuwar yara da mata.

Farah ya bayyana cewa, duk da karancin tallafin kudi daga masu bayar da gudunmawa a duniya, Jigawa ta nuna kwarewa da kirkire-kirkire wajen bunkasa ci gaba.

Sanya hannu kan wannan shirin  ya sake tabbatar da hadin gwiwarmu, wanda ke da matukar amfani ga yara da iyalai a Jihar Jigawa,” in ji shi, yana mai bukatar gwamnati ta kara ware kudade don bunkasa wadannan fannoni domin dorewar shirye-shiryen, ba tare da dogaro da tallafin kasashen waje ba.

Rediyo Najeriya ya ruwaito cewa Gwamna Namadi ya umarci dukkanin ma’aikatu, hukumomi da sassan gwamnati da abin ya shafa da su tabbatar da aiwatar da shirin.

Usman Muhammad Zaria

 

Labarai

Labarai19 hours ago

Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran

Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar. Masu...

Labarai19 hours ago

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga...

Kasuwanci20 hours ago

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a...

Kasuwanci20 hours ago

Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukaci Kiristoci da su yi tunani a kan darussa, muhimmaci, da kuma kyawawan dabi’u...

Kasuwanci20 hours ago

Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.

Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma...

Kasuwanci20 hours ago

Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa za ta gudanar da atisayen harbe-harbe ga sabbin ‘yan sanda a karamar...

Labarai20 hours ago

Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka

    Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman...

Labarai1 day ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

  Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare...

Fasaha2 days ago

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye...

Kasuwanci2 days ago

Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da...

Mafi Shahara