Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Da UNICEF Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Shirin Kare Hakkin Yara

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa da Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF sun rattaba hannu kan shirin aiki na shekaru 3 (2025-2027) da nufin inganta kare hakkin yara da mata, tare da tabbatar da rayuwarsu da ci gabansu a cikin jihar.

Taron sanya hannun, wanda aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Dutse, ya samu halartar Gwamna Malam Umar Namadi da kuma Shugaban Ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, tare da wasu manyan baki.

 

A jawabin sa, Gwamna Umar Namadi ya jaddada kyakkyawar alakar da ke tsakanin Jigawa da UNICEF tun daga kafuwar jihar a shekarar 1991.

Kamar yadda na saba fada, UNICEF ita ce tsohuwar abokiyar cigaban jihar Jigawa, wacce ke ci gaba da tallafa wa jihar tun bayan kafuwarta a 1991” in ji Gwamna Namadi.

Malam Umar Namadi ya gode wa UNICEF bisa jajircewarsa wajen samar da kudade da aiwatar da shirye-shirye da suka haifar da ci gaba a fannoni daban-daban.

Yayin da muke sanya hannu kan wannan shirin na shekaru uku, ina so in sake tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa za ta aiwatar da shi gaba daya, tare da yakinin cewa tare da hadin gwiwarmu za mu cimma burin da aka sanya a gaba.”

Ya jaddada cewa kowane yaro a Jihar Jigawa yana da damar samun kariya, tsira da rayuwa, bunkasa, samun ilimi, da kuma cika  burinsa a cikin iyali mai karfin tattalin arziki da kuma kyakkyawan yanayi.

Ya kara da cewa jihar za ta samar da dukkanin yanayin da ake bukata domin aiwatar da shirin, ciki har da sabunta dokoki, samar da kudade, da inganta hanyoyin hadin gwiwa domin tabbatar da ingancin shirin.

A nasa jawabin, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah ya jinjinawa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa jajircewarta wajen inganta rayuwar yara da mata.

Farah ya bayyana cewa, duk da karancin tallafin kudi daga masu bayar da gudunmawa a duniya, Jigawa ta nuna kwarewa da kirkire-kirkire wajen bunkasa ci gaba.

Sanya hannu kan wannan shirin  ya sake tabbatar da hadin gwiwarmu, wanda ke da matukar amfani ga yara da iyalai a Jihar Jigawa,” in ji shi, yana mai bukatar gwamnati ta kara ware kudade don bunkasa wadannan fannoni domin dorewar shirye-shiryen, ba tare da dogaro da tallafin kasashen waje ba.

Rediyo Najeriya ya ruwaito cewa Gwamna Namadi ya umarci dukkanin ma’aikatu, hukumomi da sassan gwamnati da abin ya shafa da su tabbatar da aiwatar da shirin.

Usman Muhammad Zaria

 

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara