Connect with us

Labarai

Mazauna Sabon Gero Sun Koka Kan Watsi Da Aikin Gyaran Hanyarsu

Published

on

 

Mazauna unguwar Sabon Gero, dake bayan Millennium City a Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, sun roƙi gwamnatin jihar da ta gaggauta kammala aikin gyaran titin unguwar, wanda suka ce an bar shi a cikin mawuyacin hali duk da cewa an bai wa wani kamfani aikin kusan shekara guda da ta gabata.

 

Mazauna yankin sun bayyana cewa halin da hanyar take ciki ya jefa su cikin matsanancin rayuwa, musamman mata masu juna biyu da ke tilasta musu hawa babura domin neman kulawa a wajen unguwar, kasancewar babu asibiti a yankin.

 

Ɗaya daga cikin mazauna, Rashida Shehu, wadda ke da juna biyu, ta ce ta ji rauni a lokacin da take kokarin bin hanyar zuwa gari domin kula da lafiya, inda ta roƙi gwamnati ta taimaka musu cikin gaggawa.

 

Haka kuma, rashin makarantar gwamnati a Sabon Gero ya sanya yaran mazauna yankin cikin wahala, saboda da dama daga cikinsu ba sa iya jure tafiyar neman ilimi zuwa waje.

 

Manoma kuma sun koka kan yadda rashin titin ke hana su kai kayayyakin gona kasuwa.

 

Mai unguwar Sabon Gero, Mai Anguwa Sunusi, ya bayyana cewa tun shekara guda da ta gabata aka bai wa kamfanin gyaran hanya na Think Lab aikin, amma har yanzu babu wani ci gaba da aka gani a wajen.

 

Ya roƙi gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, da ya sanya wa aikin titin muhimmanci don amfanin al’umma da jihar baki ɗaya.

A nasa bangaren, matasa ƙarƙashin kungiyar cigaban Sabon Gero sun yi barazanar gudanar da zanga-zangar lumana idan aka ci gaba da yin shiru kan aikin, inda suka ce jinkirin kammalawa ya jawo tsaikon ci gaba tare da jefa al’umma cikin haɗari da matsalolin tsaro.

 

’Yan kasuwa da masu sana’o’i a yankin sun kuma ce lalacewar titin ta rage masu ciniki, tare da hana masu saka jari daga wajen zuwa yin kasuwanci a Sabon Gero.

 

A cewar su, wannan yanayi ya sabawa alkawuran gwamnati na samar da ci gaban kowa da kowa, abin da ya sa suke jin an nuna musu wariya.

 

COV: Khadija Kubau

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara