Connect with us

Labarai

Matasan Kauru Sun Zargi Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin Tabuka Komai

Published

on

Wata kungiyar matasa, Kauru Youth Ambassadors (KYA) a karamar hukumar Kauru sun nuna matukar damuwa kan yadda Barnabas Danmaigona, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kauru a majalisar dokokin jihar Kaduna, ya gaza samar da ingantaccen wakilci tun bayan zaben sa.

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar mai taken ‘Daga Fata zuwa Yaudara’ wanda kuma Junaidu Ishaq Maisalati, ya sanyawa hannu, kungiyar ta caccaki dan majalisar kan abin da ta bayyana a matsayin mai dimama kujera kuma ɗan siyasar da ya gaza wajen gudanar da ayukka a mazabar da kuma aikin da zai amfani al’umma.

Sanarwar ta koka da yadda al’ummar Kauru suka sanya kyakkyawan fata a shugabancin Danmaigona, amma a maimakon haka, ya kasa ba marada kunya.

Har ila yau, ta yi Allah-wadai da kawancen siyasarsa da Mukhtar Chawai, wani dan siyasa da aka ce ko ake zargin bai tabuka komai a mazabarsa ba, tare da bayyana cewa irin wannan kawancen yana kashe musu gwiwa matukar gaske.

KYA ta bayyana rashin jin dadin ta a kan abin da suka kira wasu ‘yan kudaden da basu gaza dubu 5 zuwa 10 da yake rabawa jama’a a matsayin yankawa kare ciyawa domin wannan ba abin da suke tsinanawa al’ummar da yake wakilta

Saboda haka Kungiyar ta bukaci al’ummar mazabar Kauru da su tashi tsaye akan nuna halin ko-in-kula a siyasance, su nemi wakilcin da ya dace, sannan su ki yarda a ba su kyauta irin wannan da bata tsinana musu komai.

Sun yi nuni da ‘yan majalisa irin su Hon. Shehu Yunusa na Kubau, wanda rahotanni suka ce ya ba da fifiko wajen hada kai da ci gaba, a matsayin misalan yadda wakilci na gaskiya ya kasance.

Da take kira da a wayar da kan ‘yan siyasa da kuma daukar matakin gama gari, sanarwar ta kalubalanci matasa da masu kada kuri’a a Kauru da su yi wa shugabanninsu hisabi, inda ta dage cewa zabe aiki ne..

KYA ta bayyana cewa Hon. Danmaigona ya samu damarsa, kuma har yanzu jama’a na nan suna jira, ba wai kawai alkawura ba, a’a, a samu canji na zahiri.

Rel/Yusuf Zubairu

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara