Connect with us

Labarai

An katse wa majalisar dokokin Ghana lantarki saboda bashin kuɗin wuta

Published

on

Kamfanin wutar lantarki na Ghana (ECG) ya katse wutar lantarkin majalisar dokokin ƙasar a ranar Alhamis saboda gaza biyan bashin kuɗi cedi miliyan 23 da ake bin majalisar.

Wanda yawan kuɗin ya kai dalar Amurka miliyan 1.8.

Katsewar ya kawo cikas ga muhawarar da ake tafkawa a majalisar kan jawabin da shugaban kasar ya yi, inda ƴan majalisar suka rika rera taken “Dumsor, dumsor,” wato matsalar wutar lantarki.

Kafofin yada labarai na cikin gida sun ruwaito cewa duk da cewa an kunna janaretan majalisar domin samar da lantarki a lokacin, sauran sassan ginin majalisar sun kasance babu wutar a yawancin ranar.

Daraktan sadarwa na kamfanin wutar lantarki, William Boateng ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa ya dauki matakin katse wutar ne saboda ƙin amincewa da majalisar dokokin kasar ta yi na “girmama sanarwar bukatar biyan bashin”.

An dai mayar da wutar lantarkin ne bayan da majalisar ta biya cedi miliyan 13 tare da yin alkawarin sasanta sauran basukan nan da mako guda.

Daraktan sadarwa na ECG ya bayyana cewa haka za su katse wutar lantarki duk wanda ake bi bashi da kuma ƙin biyan bashin.

Kamfanin wutar lantarki na Ghana na fuskantar matsalar kudi, lamarin da ke janyo katsewar wutar lantarkin akai-akai daga abokan huldar da yake bi bashi a yayin da ake fama da ƙarancin wutar saboda kalubalen tattalin arziki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara