Connect with us

Labarai

Liverpool ta bi sahun Man Utd da Chelsea kan Neves

Published

on

Liverpool ta bi sahun Manchester United da Chelsea a fafutukar neman sayen matashin danwasan tsakiya na Benfica Joao Neves, mai shekara 19, dan Portugal, wanda kwantiraginsa ya tanadi sayar da shi a kan yuro miliyan 120. (O Jogo, daga Sport Witness)

Manchester United da Manchester City kuma suna son sayen dan bayan Bayer Leverkusen, Jeremie Frimpong mai shekara 23, dan Netherlands. (Sun)

Sannan kuma Manchester Cityn na shirin sake zawarcin danwasan tsakiya na West Ham Lucas Paqueta na Brazil mai shekara 26 a bazaran nan. (Football Insider)

Ita kuwa Leeds United tana sa ran sake sayen tsohon danwasanta na tsakiya Kalvin Phillips na Ingila a kan kusan fam miliyan 30 daga Manchester City a bazaran nan idan har ta yi nasarar komawa gasar Premier. (Sun)

Kociyan Sporting Lisbon Ruben Amorim zai duba yuwuwar tafiya Liverpool idan aka ba shi aikin, to amma zai yanke shawara ne a karshen kakar nan. (Correio da Manha)

Newcastle za ta kara azama wajen neman babban dan baya a bazaran nan sannan kuma za ta sake bai wa dan bayanta Paul Dummett sabon kwantiragi bayan da kyaftin dinta Jamaal Lascelles ya tafi jinyar kusan wata tara ta gwiwa. (Newcastle Chronicle)

Tsohon kociyan Sheffield United Paul Heckingbottom ya zama na farko a jerin wadanda Sunderland da ke gasar Championship ke son dauka a matsayin mai horarwa na dindindin na gaba. (Sun)

A shirye Barcelona take ta saurari tayi a kan Raphinha a bazaran nan domin fita daga matsin rashin kudi a bazara, to amma kuma danwasan na Brazil ba ya son barin kungiyar. (Sport)

Tottenham za ta bayar da aron Alejo Veliz, 20, ga wata kungiyar daban a kaka mai zuwa, ganin cewa matashin na tawagar Argentina ta ‘yan kasa da shekara 20 ba a sa shi wasa sosai ba a zaman aron da yake yi yanzu a Sevilla. (Fabrizio Romano)

Tottenham ta bi sahun masu son matashin danwasan tsakiya na Leeds United Archie Gray, mai shekara 18 na tawagar Ingila ta ‘yan kasa da shekara 21, wanda kuma Liverpool ma na sonshi. (Football Insider)

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai18 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai19 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai20 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi21 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara