Wasanni
Gwamnan Rivers ya karrama golan Najeriya
Gwamnan jihar River Siminalayi Fubara ya karrama golan Najeriya, Stanley Nwabali sakamakon bajintar da ya nuna gasar kofin ƙasashe Afirka ta Afcon da aka kammala makon da ya gabata.
A bikin da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar, gwamna Fubara ya bai wa golan – wanda ɗan asalin jihar ne – kyautar zunzurutun kuɗi naira miliyan 20.
Haka kuma gwamnan ya karrama shi da lambar yabo ta DSSRS, lambar yabo ta biyu mafi daraja da ake bai wa wadanda suka yi bajinta a fannoninsu, da manyan ‘yan siyasa a jihar.
Gwamnan ya kuma bai wa tawagar Super Eagles da ta samu wakilcin kocin tawagar Jose Peseiro da Finidi George kyautar naira miliyan 30, sakamakon bajintar da ƙungiyar na nuna a gasar.
Najeriya dai ta ƙare gasar a matsayi na biyu, bayan da ta sha kashi a hannun Ivory Coast mai masaukin baƙi da ci 2-1 a wasan ƙarshe.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha4 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai10 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai23 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci4 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi4 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert