Wasanni
Kwantaragin Kocin Super Eagles Na Najeriya Ta Kare
Kocin Najeriya Jose Peseiro ya sanar da kammala aikinsa da tawagar Super Eagles.
Kocin ɗan asalin Portugal ya bayyana hakan ne a shafinsa na X da aka fi sani da Twitter a ranar Juma’a.
“A jiya muka kawo ƙarshen kwantaragin da ake tsakanina da Hukumar Kwallon ƙafa ta Najeriya NFF.”
“Abin farinciki da alfahari ne koyar da tawagar Super Eagles. Watanni 22 kenan da muka kwashe muna wannan sadaukarwa da mutakuar sha’awar aikin. Muna jin mun yi abin da ya kamata,” kamar yadda kocin ya rubuta.
Ya ce yana so ya nuna godiyarsa ga tsohon shugaban hukumar NFF Amaju Pinnick da kuma na yanzu Ibrahim Gusau da Sakataren NFF Mohammed Sanusi da duka ma’aikatan hukumar da duka ‘yan wasan, wadanda duka muka yi zaman kirki da su.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha3 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai20 hours ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci3 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Labarai6 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Ilimi3 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert