Connect with us

Ilimi

Yajin Aikin NASUU da SSANU Ya Gurgunta harkikin Karatu a Jami’o’in Nujeriya

Published

on

Yajin aikin da Kungiyar ma’aikatan Jami’o’i ta kasa da suka hada da NASUU da SSANU suka fara gudanar wa ya gurgunta harkokin karatu a Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria.

Kungiyoyin ma’aikatan sun fara yajin aikin ne na kwanaki bakwai a matsayin na gargadi.

Wakilin Radio Najeriya ya bayyana cewa shugabannin Kungiyar sun rufe duk kofofin shiga Jami’ar inda dalibai da malamai na shiga harabar Jami’ar ce kawai ta hanyar taka sayyada.

Haka kuma kungiyoyin sun rufe duk wasu ayyuka a harabar dakunan kwanan dalibai da wuraren samar da ruwan sha da wutar lantarki da dakunan karatu,yayin da sauran ma’aikatan duk suka yi zaman su gida domin bin umurnin kungiyoyin.

Da yake zantawa da Radio Najeriya yayin wani tattaki da Yayan kungiyoyin suka gudanar daga ofishin Shugaban jami’ar zuwa babbar kofar shiga Jami’ar, shugaban gamayyar kungiyoyin, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar manyan ma’aikatan Jami’ar Ahmadu Bello, kwamared Mohammed Yunusa ya ce kungiyoyin sun hana gudanar da aiyukan Jami’ar ne tun ranar Litinin da aka fara yajin aikin kamar yadda uwar kungiyar ta kasa ta basu umurni.

Shugaban ya ce sun fara yajin aikin ne sakamakon rukon sakainar kashi da nuna bambanci da gwamnatin tarayya ke yi masu wajen biyan albashi da kuma gazawar gwamnati wajen cika alkawuran da ta yi a tsakanin su.

Kwamared Yunusa ya ce shugaban kasa ya bada umurnin a biya su amma wasu Jami’ai sun ki biya.

A cewar sa,Jami’an sun ki biyan su ne kasancewar basa daukar yayan kungiyoyin da muhimmanci wajen tafiyar da harkokin Jami’a,kasancewar kungiyar malaman Jami’o’i kawai suke ba muhimmanci.

Shugaban gamayyar kungiyoyin ya tunasar da gwamnati game da halin da harabar Jami’o’in za su kasance idan babu ruwa da wuta da kuma dakunan karatu da na bincike idan suka kasance a rufe.

Kwamared Mohammed Yunusa ya ce yajin aikin nasu ya yi nasara kasancewar yayan kungiyoyin biyu sun bi umurnin uwar kungiyar ta kasa.

Haliru Hamza

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai11 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai12 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci1 day ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai7 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara