Connect with us

Labarai

Gidauniyar Aliko Dangote Za Ta Yi Rabon Abinci Na Miliyoyin Naira A Najeriya

Published

on

Shahararran Attajirin nan da ya fi kowa kudi a nahiyar Afirka, Alhaji Aliko Dangote ya kaddamar da rabon abinci kyauta ga al’ummar Musulmi masu azumi su dubu goma a jiharsa ta Kano karkashin gidauniyar Aliko Dangote.

A wata sanarwa da jami’ar gidauniyar a Kano, Samira Sanusi ta fitar, ta ce za kuma a yi rabon buhunan shinkafa har guda miliyan daya da kudinsu ya haura Naira miliyan dubu goma sha uku a fadin jihohi Najeriya 36 da babban birnin tarayya Abuja domin rage radadin halin da yan kasa ke ciki.

Wannan karamci ya biyo bayan rabon biredi dubu ashirin a kullum ga mazauna Kano da kuma dubu goma sha shidda a kullum ga mazauna Legas, da gidauniyar ke yi tun lokacin annobar Korona a shekarar 2020.

Samira Sanusi ta bayyana cewa abincin da za a rika rabawa domin buda baki a wannan watan na Ramadana sun hada da dafadukar shinkafa , da shinkafa da miya , da taliya, da wake tare da kaza da naman Sa, da kuma ruwan sha.

Ta ce ana rarraba abincin ne a masallatan Juma’a, tituna, gidajen yari, da gidajen marayu, da sauran wurare a cikin birnin Kano da kewaye.

Wani wanda ya ci gajiyar abincin mai suna Musa Maikatako mazaunin garin Tarauni ya nuna jin dadinsa da wannan karamcin da ya ce ya taimaka masa wajen yin buda baki cikin sauki.

Maikatako, wanda a bayyane yake cikin farin ciki, ya ce cin abinci kyauta zai taimaka matuka ga wadanda ba sa iya samun abin da za su yi buda baki.

Maikatako ya kuma nuna godiya ga gidauniyar Dangote bisa wannan karimcin, inda ya yi addu’ar Allah Ya kara masa arziki Ya kuma ci gaba da sanya albarka a kasuwancinsa.

Wata wadda ta ci gajiyar tallafin, Hajiya Inna Tukur, ta bayyana jin dadin ta da rabon abincin, wanda a cewarta Gidauniyar Aliko Dangote ta kawo mata dauki.

A cewar ta, ta yi farin ciki da samun abinci mai daɗi kyauta a halin da ake ciki yanzu.

“Ba abin da zan ce sai  godiya gare ku da Aliko Dangote. Ina rokon Allah ya muku albarka,”

Baya ga rabon biredi da aka yi shekara 4 ana yi kyauta, Samira Sanusi ta ce ana ciyar da mabukata a Kano sama da shekaru 30 da suka shude.

A cewarta, ana hakan ne daga gidan mahaifiyarsa da ke Koki da kuma wuraren dafa abinci daban-daban.

“Shirin ciyarwa yana ciyar da mazauna Kano 10,000 a kullum da ya hada da karin kumallo, abincin rana, da kuma abincin dare” in ji ta.

USMAN MZ

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai10 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara