Connect with us

Fasaha

Wadanda Suka Kashe Dakarunmu Za Su Dandana Kudarsu — Shugaba Tinubu

Published

on

Shugaba Bola Tinubu ya ce wadanda suka kashe dakarun soji 16 a yankin Okuoma da ke Karamar Hukumar Ughelli a Jihar Delta, za su ɗanɗana kuɗarsu.

A ranar Alhamis ne wasu bata-gari suka yi wa wasu dakarun soji kisan gilla lokacin da suke kokarin sulhunta rikici tsakanin ƙabilar Okuama da Okoloba a Jihar Delta.

Bata-garin sun hallaka Kwamandan soji daya, Manjo biyu, Kyaftin daya, sojoji 12 da kuma wani mutum daya.

Tinubu cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, ya bayyana kisan a matsayin “jahilci” da cewa dole a hukunta wadanda suke da hannu a lamarin.

Ya kuma mika ta’aziyyarsa ga iyalan sojojin da aka kashe tare da bayyana aniyar gwamnatinsa na hukunta wadanda ke da hannu a kisan sojojin.

Shugaban ya ce, “Wannan lamarin, ya sake nuna irin hatsarin da ma’aikatanmu da mata ke fuskanta a bakin aiki. Ina jinjina wa jarumtarsu da jajircewarsu game da kishin kasa.

“A matsayinmu na al’umma, dole ne mu ci gaba da tunawa da kuma karrama duk wadanda ke bai wa kasarmu kariya. Dakarunmu da suka mutu a yankin Okuama sun bi sahun ‘yan mazan jiya.

“Jami’an sojojinmu su ne jigon kasarmu. Duk wani hari da aka kai musu hari ne kai tsaye ga al’ummarmu. Ba za mu yarda da wannan ɗanyen aiki ba.

“Na bai wa hedikwatar tsaro da babban hafsan soji cikakken ikon gurfanar da duk wanda aka samu da hannu wajen aikata wannan laifi.

“Gwamnatina ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai mun samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a kowane yanki na Najeriya.”

Labarai

Labarai9 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai9 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci1 day ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha1 day ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha1 day ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara