Connect with us

Labarai

CORET Ta Raba Takardun Rijista Ga Shugabannin Kungiyoyin Haɗin Kai A Kaduna

Published

on

 

Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwon Gargajiya ta Afirka (CORET) ta raba takardun rijista guda goma sha uku ga shugabannin kungiyoyin haɗin kai akan kiwon shanu a Ladduga, karamar hukumar Kachia ta Jihar Kaduna.

 

Mai kula da ayyukan CORET, Dr. Umar Hardo ne ya mika takardun a ƙarshen wani taron horaswa na kwanaki biyu da aka shirya domin wasu daga cikin shugabanni da matasan kungiyoyin haɗin gwiwa a yankin.

 

Taron horaswar, wanda ya ɗauki kwanaki biyu, CORET ta shirya shi tare da haɗin gwiwar ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka (ECOWAS) da kuma tallafin hukumar ci gaban Swiss Development Cooperation, ya samu goyon bayan wasu ƙungiyoyi da suka haɗa da Hukumar Koyar da Makiyaya ta Ƙasa, da Milk Value Chain Foundation da sauransu.

 

Dr. Umar Hardo, yace suna sa ran su ga cigaba a tsakanin dukkanin kungiyoyin hadin kai da suka samu horon musamman na samarda isasshen madara da kuma fitarda shi fiye da da.

Yace HORET tana sa ran ta ga karin samun madara da za’a rinka fitarwa daga yankin Ladugga da kuma Mai-Gatari a jihohin Kaduna da Jigawa.

 

Dr. Umar Hardo ya ce suna sa ran za’a rinka fitar da madara fiye da da, kuma tsatatace da zai kawowa wadannan kungiyoyin kuden shiga.

 

Wadda ya gabatar da kasida kuma tsohon Daraktan Ci gaban Al’umma da Kungiyoyin Haɗin Kai a Jihar Kaduna, Mista Yohanna Kabirat, yace ana sa ran mahalarta taron su iya tafiyar da Kungiyoyisu ba tareda wata matsala ba domin inganta harkar kiwon shanu da samar da madara.

 

Shi ma da yake jawabi, Shugaban Kungiyar Haɗin Gwiwar Ladduga, Salihu Yunusa, ya tabbatar da cikakken goyon bayan kungiyar ga matasa domin cimma burinsu.

 

Wasu daga cikin mahalarta sun bayyana jin daɗinsu kan horon, inda suka bayyana abubuwan da suka koya da kuma irin ƙwarewar da suka samu a lokacin taron.

Lawal Boro daga Hukumar Koyar da Makiyaya ta Ƙasa ne ya rufe taron da wata waka ta Fulatanci mai cike da ƙayatarwa da ƙarfafa gwiwa, wanda ya sa mahalarta taron suka fita da shauƙi da kwarin gwiwa.

 

COV: Adamu Yusuf

Labarai

Labarai19 hours ago

Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran

Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar. Masu...

Labarai19 hours ago

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga...

Kasuwanci19 hours ago

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a...

Kasuwanci19 hours ago

Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukaci Kiristoci da su yi tunani a kan darussa, muhimmaci, da kuma kyawawan dabi’u...

Kasuwanci19 hours ago

Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.

Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma...

Kasuwanci19 hours ago

Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa za ta gudanar da atisayen harbe-harbe ga sabbin ‘yan sanda a karamar...

Labarai20 hours ago

Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka

    Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman...

Labarai1 day ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

  Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare...

Fasaha2 days ago

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye...

Kasuwanci2 days ago

Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da...

Mafi Shahara