Connect with us

Labarai

CORET Ta Raba Takardun Rijista Ga Shugabannin Kungiyoyin Haɗin Kai A Kaduna

Published

on

 

Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwon Gargajiya ta Afirka (CORET) ta raba takardun rijista guda goma sha uku ga shugabannin kungiyoyin haɗin kai akan kiwon shanu a Ladduga, karamar hukumar Kachia ta Jihar Kaduna.

 

Mai kula da ayyukan CORET, Dr. Umar Hardo ne ya mika takardun a ƙarshen wani taron horaswa na kwanaki biyu da aka shirya domin wasu daga cikin shugabanni da matasan kungiyoyin haɗin gwiwa a yankin.

 

Taron horaswar, wanda ya ɗauki kwanaki biyu, CORET ta shirya shi tare da haɗin gwiwar ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka (ECOWAS) da kuma tallafin hukumar ci gaban Swiss Development Cooperation, ya samu goyon bayan wasu ƙungiyoyi da suka haɗa da Hukumar Koyar da Makiyaya ta Ƙasa, da Milk Value Chain Foundation da sauransu.

 

Dr. Umar Hardo, yace suna sa ran su ga cigaba a tsakanin dukkanin kungiyoyin hadin kai da suka samu horon musamman na samarda isasshen madara da kuma fitarda shi fiye da da.

Yace HORET tana sa ran ta ga karin samun madara da za’a rinka fitarwa daga yankin Ladugga da kuma Mai-Gatari a jihohin Kaduna da Jigawa.

 

Dr. Umar Hardo ya ce suna sa ran za’a rinka fitar da madara fiye da da, kuma tsatatace da zai kawowa wadannan kungiyoyin kuden shiga.

 

Wadda ya gabatar da kasida kuma tsohon Daraktan Ci gaban Al’umma da Kungiyoyin Haɗin Kai a Jihar Kaduna, Mista Yohanna Kabirat, yace ana sa ran mahalarta taron su iya tafiyar da Kungiyoyisu ba tareda wata matsala ba domin inganta harkar kiwon shanu da samar da madara.

 

Shi ma da yake jawabi, Shugaban Kungiyar Haɗin Gwiwar Ladduga, Salihu Yunusa, ya tabbatar da cikakken goyon bayan kungiyar ga matasa domin cimma burinsu.

 

Wasu daga cikin mahalarta sun bayyana jin daɗinsu kan horon, inda suka bayyana abubuwan da suka koya da kuma irin ƙwarewar da suka samu a lokacin taron.

Lawal Boro daga Hukumar Koyar da Makiyaya ta Ƙasa ne ya rufe taron da wata waka ta Fulatanci mai cike da ƙayatarwa da ƙarfafa gwiwa, wanda ya sa mahalarta taron suka fita da shauƙi da kwarin gwiwa.

 

COV: Adamu Yusuf

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara