Connect with us

Fasaha

Tarihi Da Darussa 7 Daga Yaƙin Badar Da Aka Gwabza Ranar 17, Ga Ramadan

Published

on

Yaƙin Badar ya faru ne a 17 ga watan Ramadan a shekara ta biyu bayan hijira, shi ne na farko tsakanin ƙuraishawa da Annabi (SAW), wanda a ƙarshe Allah ya bai wa Annabi (SAW) da sahabbansa nasara, a sanadiyyar abubuwan da suka wakana a yaƙin da irin sakamakon da ya haifar ya zama shi ne yaƙi mafi girma da falala a musulunci, sahabban da kuma suka halarci yakin suka zama na musamman.

Wannan yaƙin yana ɗauke da dimbin darussa wanda da al’umma za ta kiyaye su to ba ƙaramar nasara za ta cimma ba, kaɗan daga cikin waɗannan darussa akwai:

1- Muhimmancin Tsari Da Kyakkyawar Gudanarwa:

•”Taron marasa lafiya ba ya samar da ƙarfi sai dai ya samar da asibiti” [Al-Mu’utamid bin Abbad].

A tsakanin bangarorin guda biyu, ɓangaren Musulmai shi ne mafi ranuni ta fuskar yawa da kuma kayan yaƙin, domin daman can ba da niyyar yaƙin farko suka fito ba, amma a sakamakon kyakkyawan tsari na Annabi (SAW) da iya gudanarwa tun daga kan gaggauta fara isowa wurin da za a fafata (Badar), da zaɓar mafi dacewar wurin kafa sansani da kuma tsara su kansu mayakan da sauran abubuwa, musulmai suka iya cin nasara tare da cewa waɗnada suke yaƙa ɗin kafiran makka sun fi su yawa da kayan aiki da shirin yaƙin, wanda wannan yana nuna cewa ƙarancin abun hannu ko arziki ba ya hana cin nasara da samun ci gaba matuƙar al’umma ko ƙasa ko gwamnati tana da kyakkywan tsari da kuma iya gudanarwa, hakanan yawa da wadata ba ya bayar da nasara matuƙar al’umma ko ƙasa ko gwmanti ta kasance a hargiste ko lalaltaciyya ba ta tsari ba, domin taron marasa lafiya baya haɗa ƙarfi sai dai ya haɗa asibiti.

2- Muhimmancin Shawara:

•”Jama’a ta yi kuskure ya fi mutum ɗaya ya yi daidai domin in ya iya cankar daidai sau ɗaya to ya yi ta faɗawa kuskure sau da yawa, kuma ya rasa wanda zai mai uzuri” [Ibrahim Al’andalusy].

Shawara ta taka muhimiyyar rawa a nasarar Musulmai a wannan yaƙi, Annabi (SAW) duk da cewa shi ya fi kowa hankali da tinani da hangen nesa bugu da ƙarima ana saukar masa da wahayi amma duk da haka sai da Allah ya umarce shi da ya dinga shawara har abu Huraira yake cewa: banga wani mai yawaita neman shawarar sahabbansa ba sama da Manzon Allah (SAW) ba. Wanda wannan yake nuna muhimmancin shawara kuma babu wanda yake wadatuwa daga gareta komai irin iliminsa da wayewarsa da kaifin tunaninsa, hakanan shawara ita ce mabuɗin ci gaba da nasar al’umma da ita ne ake iya haɗa kan al’umma domin duk wanda ya ga ana yi da shi to wannan zai ƙara masa dangantuwa zuwa ga al’ummarsa, zai ba ta gudunmowa sosai domin yana jin cewa al’ummarsa ce ba ta wani ba, hakanan da shawara ne a kan iya naɗa wanda ya dace a idan ya dace, da kuma shawara ne ake iya kubuta daga faɗawa hatsarin ringingimu da faɗace-faɗace, don haka wajibi ne a ɗabbaƙa shawara kuma a neme ta a wurin kowa domin iya aiwatar da shawarar, iya nasarar da za a cimma ko da kuwa wannan al’umma musulma ce ko kafira.

3- Dagewa Da Addu’a Da Kuma Dogaro Da Allah:

•”Watakila nasara tana jinkiri saboda al’umma ta ƙara ƙarfin alaƙarta da Allah a yayin da take fama take shan wahala, sai ta ga ba ta da wani sai Allah. Hakan sai ya sa ta dawo kan turba da gawadabe na gaskiya, kuma idan ta samu nasara hakan ba zai sa ta karkace daga kan hanyar gaskiya da alheri da adalci ba, don ta san da su ne Allah ya bata nasara.” [ Sayyid Qudub].

Duk da cewa Annabi (SAW) ya san shi da sahabbansa su ne a kan gaskiya, kuma Allah ma ya yi mai alƙawarin nasara amma bai shantake ba, bai ce “Cin Nasara Dole” ba duk bai yi hakanan ba sai dai dagewa da dogewa a kan addu’a har sahabbansa, sannan suka fara ganin kamar abun ya yi yawa, wanda a sanadiyyar haka Allah ya saukar masa da nasararsa.

Anan zamu fahimci cewa Dogaro da Allah da kuma yin addu’a shi ne babban makamin nasara bayan mutum ya gama ɗaukar dukkanin matakai.

Rashin riko da wannan jigo yana jawowa a gagara samun nasara a rayuwa, domin ƙarfin musulmi daga Allah yake nasarar kuma ta shi ce, shi yake bayar da ita ga wanda ya ga dama, shi yasa a ko wane hali Annabi (SAW) yake ba ya ƙin addu’a, ba ya ƙin saka Allah a lamarinsa, bal kodayaushe yana ƙara nasara da ɗaukaka, yana ƙara ta’allaka da Allah.

4- Jagoranci Shi ne Ginshikin Al’ummah:

•”Idan kana son kassara ko wacce al’umma, to ka fara gusar da jagororinta ko mayar da su ƙarƙashinka”

A yaƙin Badar an kashe kafirai 70, a yaƙin Uhud kuma an kashe muslmai 70 amma a yaƙin Badar aka yanke cewa musulmai sun yi nasara a kan kafirai saɓanin yaƙin Uhud wanda duk da an yi wa musulmai ɓarna amma kuma ba a ci nasara a kansu ba, me ya bambanta waɗannan yaƙe-yaƙen biyu? Abin da ya bambanta su shi ne jagorori, kafiran Makkah sun yi asarar jagororinsu da yawa a Badar, wanda rashinsu ne yasa daular Makkah ta fara shiga rauni har aka cinyeta a ‘Fathu Makkah,’ sabanin yaƙin Uhud wanda muslmai ba su yi wannan asarar ba shi yasa ma har Abu Sufyan ya shiga tambaya ko an kashe Annabi (SAW) da Abubakar da Umar? Saboda ya san a cikin kashe waɗannan nasarar gaske take samuwa, daganan kafiran suka sake cin alwashin sai an sake haɗuwa a Badar sun ɗau fansa duk da irin barnar da suka yi uhud amma hakan bai gamsar da su ba.

Jagorori su ne ƙashin bayan kowacce al’umma, duk sanda aka yi niyyar kassara wata al’umma ko tafiya ana farawa ne daga kan jagorinta ko dai a kawar da su, ko kuma a shigar da su ƙarkashin wani ikon ta yadda za a dinga juya wannan al’umma ko tafiya yadda ake so, don haka in kana son auna lafiyar al’umma ko tafiya to ka duba jagorancinta.

5- Sadaukarwar Sahabbai:

•”Na je wurin Qaisar da Kisra da Najashi, amma banga wanda mutanesa suke girmama shi ba, suke son shi ba kamar yadda Sahabban Muhammad (SAW) Suke girmama Muhammad (SAW) ba” [Urwa bin Mas’ud Assaqafy].

A wannan yaƙin zamu ƙara gane cewa lallai sahabban Annabi (SAW) zaɓaɓɓu ne daga Allah, za mu ga yadda imani ya gama mamaye zukatansu ta yadda tun farko suka yadda suka marawa Annabi (SAW) baya a wannan yaƙin da duk wasu ma’aunan ɗan adam suna nuni da cewa ba yadda za a yi a ci nasara, amma haka suka yadda suka ƙutsa cikin halaka ba tare da la’akari da wannan ba, suna masu yaƙar iyayensu da ƴan uwansu da ƴan danginsu ba don komai ba sai don ƙasancewar imani sama yake da komai a wurinsu, sama yake da ƴan uwantaka sama yake da ƙasa, da wannan imanin da sadaukarwar ne sahabbai suka kai matsayin da suka kai.

6- Cikakken Kishi Da Soyayya Yana Ga Addinin Allah Ne:

“Da a ce a kan ƴan uwantaka ko ƙabila ko ƙasa ake kulla soyayya ko ƙiyayya da Annabi (SAW) bai barranta daga baffansa Abu-Lahab ba yaƙi Ƙuraishawa ba, da kuma barin makkah ba sai ana gina wala’ine a kan aƙida wadda tafi jini da ƙasa tsada” [ Adham Assharqawy].

A wannan yaƙin za mu ga yadda Annabi saw da sahabbansa suka yi yaƙin ƴan uwansu ƴan ƙabilarsu ƴan garinsu wanda a ma’aunin wannan zamanin hakan cin amanar ƙasa ne da rashin kishinta. A nan za mu ga cewa a musulunci babu wata alaƙa da take sama da ta addini a kansa ne musulmi yake ƙulla soyayya yake kuma kulla ƙiyayya ba tare da la’akari da ƙasa ko launi ko jinsi ba, hakanan a musulunci babu wani abu da ake kira da kishin ƙasa a ma’anarsa ta yau, kasar musulmai ita ce in da yake samun ƴancin bautar Allah ba in da Turawa suka zana a takarda ba.

7- Izzar Al’umma Tana Cikin Aiwatar Da Jihadi:

•”Jihadi yana kare al’ummah ta sanadiyyarsa ya kuma sake dunƙulewa, barinsa kuma shi yake kacaccalata ya ɗaiɗaitata” [ Abdul’Aziz Attarify].

Sakamakon yaƙin Badar Muslmai sun zama wani ƙarfi da kowa yake tsoron tinkara, ya sanya musu kwarjini a idon abokan gaba, ya kuma ɗaukaka su. Wannan shi yake ƙara nuna mana cewa lallai izzar al’umma da ɗaukakarta tana cikin aiwatar da jihadi, rashin aiwatar da shi shi zai kaita zuwa ga ƙasƙanci da halaka, kamar yadda muke gani a yau, yana daga cikin alfanun jihadi kawar da saɓani da haɗe kan al’umma domin tunkarar babban abokin gaba, hakanan da jihadi ne al’umma take ƙara samun kwanciyar hankali da yalwa da arziki shi yasa duk wanda ya karanta tarihin musulmai zai ga cewa babu sanda suka fi samun aminci da wadata sai a lokutan jihadi, babu sanda suka shiga ƙaskanci da rashin tsaro da talauci sai sanda suka saki jihadi, wanda daman wannan shi ne alƙwarin Allah.

Don haka duk da cewa yanzu ba aiwatar da jihadi ba, idan dai ba a inda suke fuskantar yaƙi ba, amma wajibi ne a sanar da al’umma, shi ya zamanto a ƙwaƙwalenta ko da ba ta da halin aiwatar da shi.

Waɗannan wasu darussane da zamu iya amfana daga yaƙin Badar. Allah ya datar da mu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara