Connect with us

Kasuwanci

CBN Ya Karawa Bankuna Jarin Da Za Su Mallaka Zuwa ₦500bn

Published

on

 

Babban Bankin Najeriya (CBN), ya kara adadin kuɗin da bankunan kasuwanci za su mallaka a matsayin jari zuwa Naira biliyan 500.

CBN, ya ce dole ne kowane banki da ke hada-hada har a ƙasashen ƙetare ya kasance yana da jarin da bai gaza Naira biliyan 500 ba.

Wannan na kunshe ne cikin wata takardar da daraktan sashen tsare-tsare da sanya ido kan ka’idojin kudi, Haruna Mustafa, ya sanya wa hannu.

CBN, ya bai wa bankunan kasuwanci da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi wa’adin watanni 24 domin cika wannan ka’ida.

Wannan wa’adi zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Afrilu, 2024, zuwa watan 31 ga Maris, 2026.

Bankunan da hada-hadarsu iya Najeriya ta tsaya, na buƙatar mafi ƙarancin jari na Naira biliyan 200 domin cikar ka’idar da CBN ya gindaya.

Kazalika, sanarwar ta bayyana cewa ya zama wajibi bankunan da ke aiki a yankunan kasar nan su zama suna da jarin da bai gaza Naira biliyan 50 ba.

 

Ya kuma bayyana cewa bankin da ke son ya rika aiki a fadin Najeriya ba tare da karbar kudin ruwa ba na bukatar jari na Naira biliyan 20.

Bankin da zai rika aiki a wani yanki guda na kasar nan, na bukatar jarin da bai gaza biliyan 10 ba.

Daka karshe, sanarwar ta bai wa bankuna shawarar hadewa domin tabbatar da samun jari mai kauri da kyautata ayyuka ga abokan hulɗarsu.

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai17 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai19 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai19 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi20 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara