Ilimi
Shugaban Kasa Na Yiwa Al’ummar Musulmi Barka Da Sallah
Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga daukacin ‘yan Najeriya da su hada kansu su dukufa wajen gina kasa mai inganci.
Shugaban ya yi wannan roko ne a lokacin da yake taya al’ummar musulmi murnar sallah karama wanda ke nuna karshen watan Ramadan, mai alfarma da ke jaddada cikakkiyar mika wuya ga Allah Madaukakin Sarki da kuma umurninsa na sadaukarwa da hidima ga bil’adama.
A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Ajuri Ngelale ya fitar, an bayyana cewa shugaban ya yi addu’ar Allah ya karba addu’o’i da sadaukarwa kowa da kowa a wannan Ramadan
Shugaban ya kuma yi fatan za a yi koyo da darussan da aka samu a wannan wata mai albarka,.
Bello Wakili/Wababe
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato