Labarai
Jirgin Sama Ya Zame Daga Kan Titinsa A Legas
Fasinjojin sun tsallake rijiya da baya, bayan jirgin saman da suka hau ya shige cikin jeji da su a Jihar Legas.
A yayin da ake ruwan sama ne wani jirgin fasinja mallakin kamfanin Dana Air ya zame daga kan titinsa a filin jirgi na Murtala Muhammad da ke Legas, sannan ya ci kasa a cikin jeji.
Hakan ya sa fasinjojin ficewa cikin gaggawa don tsira da rayuwarsu da kuma guje wa abin da ka iya biyowa baya.
Bidiyon abin da ya faru da fasinjojin suka ɗauka bayan sun tsallake rijiya da baya ya nuna tayar gaban jirgin ta nutse a kasa a cikin ciyayi.
Zuwa lokacin hada wannan rahoti dai hukumomi ko kamfanin Dana Air ba su ce komai kan lamarin ba.
Haka zalika babu bayanin cewa wani ya samu rauni ko kuma asarar rai ba.
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar