Connect with us

Kasuwanci

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3

Published

on

Gwamnatin jihar Kwara ta binne duk wani naman dabbobin da ake zargi yana dauke da guba don gujewa sayarwa mutane a  kusa da Kwalejin Kolejin Koyon Larabci da Shari’ar Musulunci ta Jihar Kwara (CAILS) da ke Ilorin.

 

Hakan ya biyo bayan wasu matakan da aka dauka na hana mutane cin naman dabbobin  da ake zargin yana dauke da  guba a jihar.

 

A cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar ma’aikatar noma da raya karkara, Madam Funke Sokoya ta fitar, ta ce gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki sun amince da dakatar da ayyukan yanka dabbobi har na tsawon kwanaki uku domin a samu damar yin feshin magani a  Mahautar don dakile duk wata cuta da ke gurin.

 

Sanarwar ta ce binciken farko ya nuna cewa mummunan lamarin ya faru ne sakamakon kiwo da gurbatacciyar ciyawa da ke kewaye da yankin.

 

Sanarwar ta bayyana cewa, ma’aikatar za ta kara sanya ido a sauran Mayanku  daban-daban na jihar domin tabbatar da tsaftar muhalli.

 

A nasa jawabin, Daraktan Kula da Dabbobi, Dokta Olugbon Saliman, ya ce, za a rage yawan Mahauta da ba na gwamnati ba zuwa matakin da ma’aikatar za ta iya sarrafawa.

 

Ya ce duk wata Mayanka  da ba ta bi ka’idojin gwamnati ba game da  tsafta, za a rufe ta.

 

Ali Muhammad Rabi’u

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara