Labarai
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dauki Matakan Kawar Da Nama Me Guba A Kasuwannin Jihar
Gwamnatin jihar Kwara ta ce ta samar da matakan kare lafiyar jama’a a daidai lokacin da ake ta yayata jita-jitar sayar da naman Sa me guba a wasu kasuwannin jihar.
A cikin wata sanarwa da kwamishinar lafiya ta jihar, Dr. Amina Ahmed El-Imam ta fitar, ta ce an kafa wata babbar tawaga don sanya ido kan lamarin.
Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnatin jihar ta kwace dukkan naman da ake zargi domin yin gwaji akan su, bayan wata ganawa da aka yi da masu ruwa da tsaki naKasuwar.
Sanarwar ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, yayin da ake ci gaba da bincike don tabbatar da gaskiyar lamarin.
Sanarwar ta kuma yabawa shugabannin kasuwar bisa hadin kan da suka bayar don shawo kan lamarin.
Sama da shanu talatin da uku 33 ake zargin sun mutu sakamakon guba a yankin Atere da ke Ilọrin.
An kuma yi zargin cewa an yanka matattun dabbobin ne aka raba wa mahauta domin sayarwa a kasuwanni.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar