Connect with us

Labarai

An Gudanar Da Taron Bita Kan Dashen Koda A Kano

Published

on

Shugaban Jami’ar Bayero da ke Kano Farfesa Sagir Adamu, ya ce asibitin koyarwa na Aminu Kano ya gudanar da dashen koda sama da dari daya daga shekarar 2002 zuwa yanzu.

 

Farfesa Sagir ya bayyana hakan ne a yayin wani taron bitar dashen koda na yini uku da Asusun Tallafawa Manyan Makarantu na Kasa TETFUND ya shirya a asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH).

Shugaban jami’ar wanda mataimakinsa na sashen gudanarwa Farfesa Mahmud Sani  ya  wakilce shi, ya bayyana cewa, Asibitin Aminu Kano na daya daga cikin asibitocin koyarwa na Arewa da suka fara aikin dashen koda shekaru 20 da suka gabata.

Ya yabawa Asusun na TETFUND bisa kaddamar da taron shirin a AKTH tare fatan ganin dorewarsa da kuma fadada shi zuwa wasu asibitocin.

A jawabinsa Babban Daraktan Kula da Lafiya na asibitin, Farfesa Umar Gajida, ya yi nuni da cewa Asusun TETFUND ya yi ayyuka da dama a fannin dashen Koda.

 

Shugaban ’yan kwangilar da suka samar da kayan aikin dakin gwaje-gwaje Alhaji Umar Ali, ya jaddada cewa an kashe sama da Naira miliyan dari biyu don sayan kayan aikin  dashen Koda.

Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yi alkawarin yin amfani da ilimin da suka samu ta hanyar da ta dace.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa an zabo mahalarta taron ne daga asibitocin koyarwa guda shida a fadin jihohin Kano da Bauchi da Filato da Maiduguri da Abuja da kuma Kaduna, inda za a yi dashen koda har guda uku a karshen taron bitar domin likitocin su kara fahimtar aikin dashen.

Khadija Aliyu

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai2 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi2 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara