Labarai
An Gudanar Da Taron Bita Kan Dashen Koda A Kano
Shugaban Jami’ar Bayero da ke Kano Farfesa Sagir Adamu, ya ce asibitin koyarwa na Aminu Kano ya gudanar da dashen koda sama da dari daya daga shekarar 2002 zuwa yanzu.
Farfesa Sagir ya bayyana hakan ne a yayin wani taron bitar dashen koda na yini uku da Asusun Tallafawa Manyan Makarantu na Kasa TETFUND ya shirya a asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH).
Shugaban jami’ar wanda mataimakinsa na sashen gudanarwa Farfesa Mahmud Sani ya wakilce shi, ya bayyana cewa, Asibitin Aminu Kano na daya daga cikin asibitocin koyarwa na Arewa da suka fara aikin dashen koda shekaru 20 da suka gabata.
Ya yabawa Asusun na TETFUND bisa kaddamar da taron shirin a AKTH tare fatan ganin dorewarsa da kuma fadada shi zuwa wasu asibitocin.
A jawabinsa Babban Daraktan Kula da Lafiya na asibitin, Farfesa Umar Gajida, ya yi nuni da cewa Asusun TETFUND ya yi ayyuka da dama a fannin dashen Koda.
Shugaban ’yan kwangilar da suka samar da kayan aikin dakin gwaje-gwaje Alhaji Umar Ali, ya jaddada cewa an kashe sama da Naira miliyan dari biyu don sayan kayan aikin dashen Koda.
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yi alkawarin yin amfani da ilimin da suka samu ta hanyar da ta dace.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa an zabo mahalarta taron ne daga asibitocin koyarwa guda shida a fadin jihohin Kano da Bauchi da Filato da Maiduguri da Abuja da kuma Kaduna, inda za a yi dashen koda har guda uku a karshen taron bitar domin likitocin su kara fahimtar aikin dashen.
Khadija Aliyu
-
Labarai3 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai2 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai4 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana