Connect with us

Ilimi

Sasantawa ce Jigon Kowane Irin Zaman Lafiya – Dr Joseph

Published

on

Cibiyar tabbatar da zaman lafiya da sasantawa ta ce tana ganawa da manyan abokan hulda da masu ruwa da tsaki a duk fadin kasar a wani yunkuri na samar da zaman lafiya ba tare da nuna banbancin addini ko kabalancin ba.

 

Babban daraktan cibiyar, Dr. Joseph Ochogwu ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a jihar Sokoto.

 

Mista Joseph Ochogwu ya ce cibiyar da ke karkashin ma’aikatar harkokin waje ta tarayya a halin yanzu tana hada kungiyoyin farar hula, hukumomin tsaro, malamai, kungiyoyin addini a kokarinta na tattauna hanyoyin da ake bukata da kuma samar da hanyoyi domin samun dauwamammen zaman lafiya a kasa.

 

Shugaban ya ce an dauki matakin ne da nufin inganta fahimtar juna tsakanin jama’a da dukkan gwamnatocin jihohi da nufin samar da ribar dimokuradiyya don samun ci gaba mai dorewa.

 

Ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta bukaci goyon bayan jama’a domin ba gwamnati damar samar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban tattalin arziki da tsaro a kasar nan.

 

Mista Joseph Ochogwu ya kara da cewa, za a iya cimma hakan ta hanyar samar da zaman lafiya da sasanta rikici tsakanin gwamnatocin jihohi da al’ummomi a fadin kasar nan.

 

Ya kara da cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yana ajandar muhimman abubuwa guda takwas da suka ta’allaka gaba daya kan zaman lafiya, tsaro da ci gaban tattalin arziki.

 

NASIR MALALI/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai2 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi2 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara