Ilimi
Sasantawa ce Jigon Kowane Irin Zaman Lafiya – Dr Joseph
Cibiyar tabbatar da zaman lafiya da sasantawa ta ce tana ganawa da manyan abokan hulda da masu ruwa da tsaki a duk fadin kasar a wani yunkuri na samar da zaman lafiya ba tare da nuna banbancin addini ko kabalancin ba.
Babban daraktan cibiyar, Dr. Joseph Ochogwu ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a jihar Sokoto.
Mista Joseph Ochogwu ya ce cibiyar da ke karkashin ma’aikatar harkokin waje ta tarayya a halin yanzu tana hada kungiyoyin farar hula, hukumomin tsaro, malamai, kungiyoyin addini a kokarinta na tattauna hanyoyin da ake bukata da kuma samar da hanyoyi domin samun dauwamammen zaman lafiya a kasa.
Shugaban ya ce an dauki matakin ne da nufin inganta fahimtar juna tsakanin jama’a da dukkan gwamnatocin jihohi da nufin samar da ribar dimokuradiyya don samun ci gaba mai dorewa.
Ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta bukaci goyon bayan jama’a domin ba gwamnati damar samar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban tattalin arziki da tsaro a kasar nan.
Mista Joseph Ochogwu ya kara da cewa, za a iya cimma hakan ta hanyar samar da zaman lafiya da sasanta rikici tsakanin gwamnatocin jihohi da al’ummomi a fadin kasar nan.
Ya kara da cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yana ajandar muhimman abubuwa guda takwas da suka ta’allaka gaba daya kan zaman lafiya, tsaro da ci gaban tattalin arziki.
NASIR MALALI/Wababe
-
Labarai3 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi4 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha4 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai4 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai2 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar