Labarai
‘Yansandan Jihar Filato Zasu Koya Darasi Ga Masu Daukar Hukunci Ba Tare Da Bincike Ba
Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Filato, ta sha alwashin ba da misali da masu yanke hukunci da kansu ba tare da barin doka ta yi aikin ta ba.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Filato, CP Emmanuel Adesina ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Jos yayin da suka kama wasu manyan mutane tara (9) da ake zargi da hannu wajen garkuwa da mutane da wasu laifuka daban-daban.
Ku tuna cewa a wasu lokutan a cikin watan Agustan wannan shekara ta 2025, an kashe jami’an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) a karamar hukumar Bassa sakamakon aikata irin wannan danyen aiki.
An bayyana cewa dan sandan ya tafi bakin aiki ne, inda ya zakulo wanda ake zargi da gudu sannan ya kama mai laifin, sai ya fara ihun barawo…. barawo….sai ga jama’a sun kashe jami’in har lahira ba tare da basu damar bayyana kansa ba.
Rundunar ‘yan sandan jihar Filato, CP, wadda ya yi kakkausar suka ga irin wannan aikin, ya ce sun kama mutane da dama da ake zargi da aikata laifin.
Ya kuma bayyana dalilin da ya sa aka kama wadanda ake zargi da yin garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka a wurare daban-daban a fadin jihar.
Ya kuma bukaci ‘yan jihar Filato da su kasance masu taka-tsan-tsan tare da baiwa jami’an tsaro sahihin bayanai masu inganci da za su bankado masu mugun nufi da jihar Filato da Najeriya baki daya.
DORCAS GWANI JOS.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
