Connect with us

Ilimi

Abin Da Ya Sa Ba A Cika Satar Ɗalibai Ba A Borno — Zulum

Published

on

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya bayyana riko da tsarin nan na “safe school initiative” a matsayin sirrin da ya sa ba cika samun labarin satar ‘yan makaranta ba a jihar.

Tsarin na “safe school initiative” dai wani shiri ne da ya wajabta gina katanga da daukar ma’aikata masu ɗauke da makamai domin kare lafiya da dukiya a makarantu.

Zulum ya bayyana ne Fadar Gwamnatin Najeriya jim kaɗan bayan fitowarsa daga wani taro na shuwagabanni a kasar nan.

Zulum ya ce “Mun kai akalla shekara bakwai zuwa takwas da ƙaddamar da tsarin ‘Safe School Initiative ’ a Jihar Borno.
“Kusan duk makarantunmu na da katanga, mun gayyaci sojoji da ’yan sanda aikin tsare ɗalibai da makarantunmu.”

Zulum ya kara da cewa “Mun ɗauki ’yan banga da ’yan sa-kai suna taimaka wa jami’an tsaron kasar nan yadda ya kamata wurin tabbatar da tsaro a makarantun Jihar Borno.”

Gwamna Zulum ya jinjina wa jami’an tsaron bisa ƙoƙarin da ya ce suna yi wurin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a Borno da sauran sassan kasar nan.

Jihar Borno dai ɗaya ce daga cikin jihohin da suka sha fama da bala’in ta’addancin kungiyar Boko Haram da ISIS masu tada ƙayar baya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Fasaha20 mins ago

Gwamnan Kaduna Ya Kaddamarda Sabbin Ajujuwa A Zaria

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya kaddamar da rukunin ajujuwa 18 a makarantun Basic Education guda biyu dake karamar hukumar...

Fasaha40 mins ago

Shugaban Kasa Ya Kaddamar Sabon Birnin Kasuwanci A Abuja

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da samarda wani da za a samar don gudanarda harkokin kasuwanci a cikinsa da...

Labarai1 hour ago

Kungiyar CAN Ta Rasa Mata Shida A Hadarin Mota A Taraba

An bayyana cewa wasu ’yan kungiyar mata ta kungiyar Kiristoci ta Najeriya (WOWICAN) su shida ne suka rasa rayukansu a...

Labarai1 hour ago

‘Yan Sakai Jihar Taraba Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Yi Garkuwa

Rundunar ‘yan banga ta Najeriya (VGN) reshen jihar Taraba ta yi nasarar ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa...

Ilimi2 hours ago

Talatar Nan Jirgin farko na Maniyatan jihar Kwara Zai Tashi

An dage tashin jirgin farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon na kasa da kasa na Ilorin don...

Labarai2 hours ago

HARIN MASALLACIN KANO: Obi Ya Ziyarci Wadanda suka Mutu

  Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya ziyarci wadanda kona masallacin Kano...

Labarai2 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Ta Yi Kiran A Yiwa Mijinta Addu’a

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce addu’a ita ce ginshikin duk wani shugabanci mai nasara, don...

Labarai2 hours ago

Gwamnatin Kano Ta Rufe Asibitin Kwanar Ganduje A Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta rufe tare asibitin Kwanar Ganduje dake unguwar Sharada Karamar Hukumar Kano Municipal.   Babban daraktan hukumar...

Labarai3 hours ago

Shugaban Iran Ebrahim Raisi Ya Rasu A Hatsarin Jirgi

Jami’an Iran sun ce Shugaba Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar, Hossein Amir-Abdollahian sun rasu a wani hatsarin jirgin...

Labarai14 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Mafi Shahara