Labarai
Kwamandojin Boko Haram 2 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno
Wasu kwamandojin Boko Haram biyu, Ibrahim Muhammed da Auwal Muhammed, sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF da ke Monguno a Jihar Borno.
Rundunar MNJTF ta hada da kasashe da dama da suka hada da rundunar sojin kasashe irin su Benin, Kamaru, Chadi, Nijar da muma Nijeriya.
Rundunar tana da hedikwata a N’Djamena, babban birnin kasar Chadi kuma tana yaki da ta’addancin Boko Haram.
Shugaban yada labaran rundunar, Lafkanar Kanal Abubakar Abdullahi ne, ya bayyana a ranar Talata, inda ya bayyana cewa Kwamandojin biyu sun mika wuya ne bayan sun shafe fiye da shekara 10 suna aikata ta’addanci.
Abdullahi ya kuma bayyana cewa, a yayin bincike, maharan biyu sun amince za su taimaka wa rundunar da bayanai don samun nasarar dakile abokan aikinsu.
“An kwato makamai daga hannun ‘yan ta’addan da suka mika wuya.
“Kayan da aka kwato daga hannun Ibrahim Muhammed sun hada da bindigogi kirar AK-47 guda biyu, harsashin AK-47 guda uku da wayar hannu guda daya.
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai6 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai4 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha22 hours ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci19 hours ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Labarai6 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas
-
Fasaha22 hours ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet