Connect with us

Labarai

Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Kai Samame Gidan Kakakin Majalisar Afrika Ta Kudu

Published

on

Masu bincike sun kai samame gidan shugabar majalisar dokokin kasar Afrika ta Kudu, bisa zargin da ake mata na cin hanci da rashawa, wanda hakan ya sanya ‘yan adawa suka bukaci ta yi murabus.

Hakan dai na zuwa ne watanni biyu kafin babban zaben kasar, a dai-dai lokacin da ake ci gaba da kai wa ‘ya’yan jam’iyar da ke mulki ta ANC samame, bisa zarginsu da aikata badakalar cin hanci da rashawa.

 

Hukumar da ke yaki da cin hancin da rashawa ta kasar dai ta tabbatar da cewa, wata babbar tawagar jami’anta sun kai samamen ne don gudanar da binciken a gidan shugabar majalisar Nosiviwe Mapisa-Nqakula da ke Johannesburg.

 

Majalisar dokokin kasar dai ta ce wannan binciken da ake yi wa Mapisa-Nqakula, na da alaka da zargin badakala da ake mata lokacin ta na ministar tsaron kasar.

 

Mapisa-Nqakula ta rike mukamin ministar tsoron kasar ne tsakanin shekarar 2014 zuwa 2021, kafin daga bisani aka nadata kakakin majalisar dokokin kasar, da hakan ya fuskanci suka daga bangaren ‘yan adawa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai6 mins ago

HARIN MASALLACIN KANO: Obi Ya Ziyarci Wadanda suka Mutu

  Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya ziyarci wadanda kona masallacin Kano...

Labarai25 mins ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Ta Yi Kiran A Yiwa Mijinta Addu’a

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasir Idris, ta ce addu’a ita ce ginshikin duk wani shugabanci mai nasara, don...

Labarai43 mins ago

Gwamnatin Kano Ta Rufe Asibitin Kwanar Ganduje A Kano

Gwamnatin jihar Kano, ta rufe tare asibitin Kwanar Ganduje dake unguwar Sharada Karamar Hukumar Kano Municipal.   Babban daraktan hukumar...

Labarai1 hour ago

Shugaban Iran Ebrahim Raisi Ya Rasu A Hatsarin Jirgi

Jami’an Iran sun ce Shugaba Ebrahim Raisi da ministan harkokin wajen ƙasar, Hossein Amir-Abdollahian sun rasu a wani hatsarin jirgin...

Labarai12 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Mafi Shahara