Labarai
Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Kai Samame Gidan Kakakin Majalisar Afrika Ta Kudu
Masu bincike sun kai samame gidan shugabar majalisar dokokin kasar Afrika ta Kudu, bisa zargin da ake mata na cin hanci da rashawa, wanda hakan ya sanya ‘yan adawa suka bukaci ta yi murabus.
Hakan dai na zuwa ne watanni biyu kafin babban zaben kasar, a dai-dai lokacin da ake ci gaba da kai wa ‘ya’yan jam’iyar da ke mulki ta ANC samame, bisa zarginsu da aikata badakalar cin hanci da rashawa.
Hukumar da ke yaki da cin hancin da rashawa ta kasar dai ta tabbatar da cewa, wata babbar tawagar jami’anta sun kai samamen ne don gudanar da binciken a gidan shugabar majalisar Nosiviwe Mapisa-Nqakula da ke Johannesburg.
Majalisar dokokin kasar dai ta ce wannan binciken da ake yi wa Mapisa-Nqakula, na da alaka da zargin badakala da ake mata lokacin ta na ministar tsaron kasar.
Mapisa-Nqakula ta rike mukamin ministar tsoron kasar ne tsakanin shekarar 2014 zuwa 2021, kafin daga bisani aka nadata kakakin majalisar dokokin kasar, da hakan ya fuskanci suka daga bangaren ‘yan adawa.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United