Labarai
Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani
Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar ranar Talata, in ji hukumomin Faransa.
Masu gadin teku sun ce mutanen da lamarin ya rutsa da su na koƙarin zuwa Birtaniya ne cikin wani kwale-kwale maƙare da ƴan ci-rani 110.
Tuni aka ƙaddamar da aikin ceto domin zaƙulo mutanen da suke cikin ruwa.
Sakataren harkokin cikin gida na Birtnaiyam James Cleverly ya ce: “Dole ne a magance wannan bala’i. Ba zan amince da halin da ake ciki ba da ke janyo asarar rayuka.”
Mista Cleverly ya ce gwamnatin Birtaniya tana yin duk mai yiwuwa na kawo ƙarshen miyagu masu safarar mutane.”
Tun farko, majalisar dokokin Birtaniya ta amince da ƙudirin neman tura masu neman mafaka a Birtaniya zuwa Rwanda bayan shafe watanni ana ƙiƙi-ƙaƙa a kai.
Kudurin ya ayyana Rwanda a matsayin kasar da ba ta da wata matsala dangane da ƙudurin, bayan da kotun ƙolin Birtaniya ta zartar a watan Nuwamba cewa shirin na gwamnati ya saba doka.
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar