Connect with us

Labarai

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Published

on

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar ranar Talata, in ji hukumomin Faransa.

Masu gadin teku sun ce mutanen da lamarin ya rutsa da su na koƙarin zuwa Birtaniya ne cikin wani kwale-kwale maƙare da ƴan ci-rani 110.

Tuni aka ƙaddamar da aikin ceto domin zaƙulo mutanen da suke cikin ruwa.

Sakataren harkokin cikin gida na Birtnaiyam James Cleverly ya ce: “Dole ne a magance wannan bala’i. Ba zan amince da halin da ake ciki ba da ke janyo asarar rayuka.”

Mista Cleverly ya ce gwamnatin Birtaniya tana yin duk mai yiwuwa na kawo ƙarshen miyagu masu safarar mutane.”

Tun farko, majalisar dokokin Birtaniya ta amince da ƙudirin neman tura masu neman mafaka a Birtaniya zuwa Rwanda bayan shafe watanni ana ƙiƙi-ƙaƙa a kai.

Kudurin ya ayyana Rwanda a matsayin kasar da ba ta da wata matsala dangane da ƙudurin, bayan da kotun ƙolin Birtaniya ta zartar a watan Nuwamba cewa shirin na gwamnati ya saba doka.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara