Labarai
Za a bada tallafin kayan Miliyan 250 ga wadanda rikici ya shafa a Jos
Asusun tallafawa wadanda wata masifa ta Shafa ya bada gudummuwar kayaking da kudin su ya kai naira miliyan 250 ga al’unmar kananan hukunomin da jihar Plateau da suka hada da Riyom, Bassa da barikin Ladi.
Gwamnan jihar Plateau Caleb Mutfwang ya fada wajen kaddamar da bada tallafin cewa, zasuyi dukkanin abin da zasu iya don tabbatar tsaron lafiya da dukiyar al’umma.
Asusun Wanda ke karkashin jagorancin Theophilus Danjuma na masu zaman kansu ne da ke mayarda hankali wajen bada tallafin ilimi, tsaftar muhalli da ruwansha da dai sauransu.
Manufar ita ce dai karfafa al’ummomin kananan hukumomin Bassa Riyom da Barikin Ladi da wannan masifar ta Shafa.
Kayayyakin da aka bada tallafi sun hada da kayayyakin abinci da na karatu.
Gwamnan Jihar Plateau yace wata manufar su ita ce mayarda al’ummomin da aka raba da gidajen su na iyaye da kakanni don su ci gaba da noma, saboda gwamnati ba tada nufin ajiye su a sansanonin ‘yan gudun hijira.
Gwamnan ya Kuma godewa wadanda suka bada wannan tallafi tare da bayyana cewa ya bada umurnin ga sakataren Gwamnatin jihar da ya kafa wani kwamiti mai zaman kansa da zai bibiyi dukkanin abubuwan da za ayi don tabbatar da gaskiya da adalci wajen rabon kaya.
Jami’ar ayukka ta Asusun Mrs. TOYOSI Akenrele Ogunsiyi ta bayyana cewa suna sane da duk wani kalubale da ake fuskanta, sai dai ba za ta iya Kamala aikin Nan.
Shugabar asusun wacce ta bayyana al’ummar jihar Plateau a matsayin masu hazaka tace zasu talafawa dukkanin masu kasuwanci domin bunkasa harkokin su.
Mrs. Akenrele Ogunsiyi tace zasu mayarda hankali wajen ganin cewa sunyi aiki da duk Wanda ya rike aikinsa da gaskiya tare da hukunta wadanda suka kasa yin aikin da aka sa su
Shi Kuma shugaban hukunar bada agajin gaggawa na jihar Mr. Sunday Abudu ya bada tabbacin cewa za ayi adalci wajen rabon kayan tallafin.
Josiah Buzum/Shafii Wababe
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United