Labarai
An umarci ma’aikatan gwamnati su rinƙa motsa jiki duk mako a Uganda
Gwamnatin Uganda ta umarci dukkan ma’aikatanta da su rinƙa ware sa’a biyu a duk mako suna motsa jiki domin su kasance cikin ƙoshin lafiya.
Gwamnatin ta ce an bayar da umarnin ne domin ceton rayukan ma’aikatan da kuma rage musu kamuwa da wasu cutuka da suka jiɓanci rashin motsa jiki.
Cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, gwamnatin ta ce an ɗauki wannan matakin ne domin a canja yanayin tsarin rayuwar ma’aikata da kuma rage haɗarin kamuwa da cutuka a ƙasar.
Gwamnatin ta ɗauki wannan matakin ne bayan wani bincike da hukumar lafiya ta ƙasar ta gudanar wanda ya nuna an samu ƙaruwar masu ƙiba sosai a ƙasar da ya kai daga kashi 17 cikin 100 zuwa 26 cikin 100.
Ba wannan ne karon farko da gwamnatin ta Uganda ta fara bayar da irin wannan umarni ba,ko a 2018 ma an yi wasu abubuwa makamantan haka.
-
Labarai6 days ago
Wajibi Ne a kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kano Nan da Watanni 14 – FG
-
Labarai5 days ago
Hukumar Shige da Fice Ta Gargadi Jama’a Kan Sabuwar Kungiya Achad Life Mission
-
Labarai2 days ago
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Samar Da Masauki Na Alfarma Ga Alhazan Jihar
-
Kasuwanci6 days ago
Na Biya Dala Dubu 3 Don a Asirce Mijina Ya Mayar da Auren Mu – Bose
-
Labarai4 days ago
Gwamnatin Neja Ta Haramtawa Motocin Da Suka Fito Daga Hanyar Maje Bin Gadar Dikko
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jihar Kano Ta Dawo Da Ayyukan Ma’aikatar Yada Labarai
-
Labarai5 days ago
Majalisar Dattijai Ta Bukaci Karfafa Jarin Bankin Lamunin Gidaje Na Tarayya
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Nijar ta soke biyan kudaden PTA a Makarantun Gwamnati