Labarai
An umarci ma’aikatan gwamnati su rinƙa motsa jiki duk mako a Uganda
![](https://radionigeriakaduna.gov.ng/hausa/wp-content/uploads/2024/03/59f9dfea-8f3a-4b8b-83b2-2ebd407a9374.jpg)
Gwamnatin Uganda ta umarci dukkan ma’aikatanta da su rinƙa ware sa’a biyu a duk mako suna motsa jiki domin su kasance cikin ƙoshin lafiya.
Gwamnatin ta ce an bayar da umarnin ne domin ceton rayukan ma’aikatan da kuma rage musu kamuwa da wasu cutuka da suka jiɓanci rashin motsa jiki.
Cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, gwamnatin ta ce an ɗauki wannan matakin ne domin a canja yanayin tsarin rayuwar ma’aikata da kuma rage haɗarin kamuwa da cutuka a ƙasar.
Gwamnatin ta ɗauki wannan matakin ne bayan wani bincike da hukumar lafiya ta ƙasar ta gudanar wanda ya nuna an samu ƙaruwar masu ƙiba sosai a ƙasar da ya kai daga kashi 17 cikin 100 zuwa 26 cikin 100.
Ba wannan ne karon farko da gwamnatin ta Uganda ta fara bayar da irin wannan umarni ba,ko a 2018 ma an yi wasu abubuwa makamantan haka.
-
Labarai7 days ago
Al’ummar Kauru Na Cikin Zullumi Bayan Lalacewar Gadar Da Ta Hadasu Da sauran Al’ummomin Jihar Kaduna
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Harkar Noma A Yobe
-
Labarai2 days ago
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
-
Kasuwanci4 days ago
An Shawarci Matasan Jihar Niger Su Guji Shiga Zanga-Zangar Babu Gaira Babu Dalili
-
Labarai4 days ago
Zanga Zanga: Gwamnati Ta Baiwa Matasa Tabbacin Daukan Bukatun Su Da Mahimmanci
-
Labarai3 days ago
‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Za Ta Samar Da Kananan Jiragen Ruwa A Kananan Hukumomi 3
-
Labarai4 days ago
Taurarin Finafinan Hausa Na Alhinin Rasuwar Sulaiman Alaka