Connect with us

Ilimi

Majalisar Wakilai Na Bukatar Sanin Dalilin Da Ke Sa Jirgin Kasan Abuja Kaduna Ke Goce Hanya

Published

on

Majalisar Wakila zata gayyaci Ministan sufuri domin ya yima yan Najeriya bayanin abinda ya janyo jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja yake sauka daga kan laying dogo Wanda hakan Kan iya haifar da mummunan hadari ga rayuwar fasinjoji.

jirgin bukaci a gudanar da bincike kan musabbin abin da ke sa jirgin kasan Abuja- Kaduna ke karkacewa daga layin dogo wanda Kan iya haifar da mummunan hatsari ga rayuwar fasinja.

Hakan ya biyo bayan Kudurin gaggawa ne da Danmajalisa Mai wakilar mazabar Makarfi Kudan a Jihar Kaduna Alhaji Uamr Shehu Ajilo ya gabatar a zauren Majalisar da aka amince dashi.

Da yake gabatar da kudirin Alhaji Umar Shehu Ajilo ya koka ganin yadda Jirgin ke yawan turgudewa daga layin dogo inda hakan ka iya shafar sufirin jiragen kasa duk da irin gudunmawar da sashen ke bayarwa wajen tsaron lafiya da dukiliyar al’umma baki daya.

To amma yanda jirgin kasan Kaduna – Abuja yake yawan karkacewa daga hanyarsa na haifar da barzana ga rayuwar fasinjoji, lamarin ya Sanya bukatar mu hadakai domin daukar mataki.

Ya ce ganin yadda jirgin kasan yake jigilar fasinjoji da kaya da dama daga Kaduna zuwa Abuja, sannan yana bada gagarumar gudunmawa a fannin ci cigaban tattalin arziki da alummar Najeriya akwai bukatar majalisar ta sauki mataka gaggawa son gudun jefe al’umma cikin halin ni ‘yasu.

Alhaji Umar Ajilo, ya Kara da cewa abin takaici ne yadda jirgin kasan ke yawan sauka daga layin dogo, na baya bayan nan shi ne wanda ya faru a tashar jirgin kasa ta garin Asha da ke Babban birnin tarayya Abuja inda ya bar fasinjoji kara zube bayan Wanda ya faru a makonni biyu da suka gabata.

Ya cigaba da cewa wajibi ne Majalisar Wakilai ta gudanar da bincike domin gani dalilan da suka sa Jirgin kasan Kaduna-Abuja ne kadai yake fuskantar irin wannan Matsalar domin kare aukuwar lamarin anan gaba.

Da take amincewar da kudurin Majalisar ta umarci kwamitinta ya gayyaci ministan sufiri da sauran Jagororin a bangaren sufurin jiragen kasan da su zo su yi mata bayani don lalubo hanyoyin maganve sake faruwar hakan a nan gaba.

Ana sa ran Kwamitin ya gudanar da binciken sa cikin makonni hudu da gabatar da rahoton sa a zauren majalisar don daukan Madaki na gaba.

COV : TSIBIRI

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai1 day ago

Ziyarar Shugaba Tinubu Zuwa China Ta Yi Nasara

  Ziyarar Shugaba Tinubu zuwa China Ta Yi Nasara, da kuma Shaida Wa ‘Yan Najeriya Mazauna China, Yi Alkawarin don...

Labarai2 days ago

Sabon Tsarin Albashi: Majalisar Kano Ta Amince da Karin Kasafin Naira Biliyan 99

Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙarin kasafin kudi na N99bn da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Musanta Jita-Jitar Bayar Da Kudi Ga ‘Yan Ta’adda

  Gwamnatin Jihar Zamfara tayi watsi da jita-jitar da ke yawo cewar tana shirin bayar da kudi ga wasu sanannun...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Dauki Matakan Gaggawa Don Wadata Man Fetur da Farashinsa

  Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Ɗauki Matakai Masu Ƙarfi don Magance Samuwar Man Fetur da Farashi a Faɗin Najeriya A...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nemi Hadin Gwiwar Afirka da China Don Bunkasa Tattalin Arziki

  Shugaba Bola Tinubu ya yi kira da a ci gaba da hadin kai tsakanin Afrika da Sin, yana mai...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya ta Amince da Tsare-tsare Don Yakar Rashin Abinci Mai Gina Jiki

  Daga: Bello Wakili Ministan Tsare-tsare na Lafiya da Walwala ta Jama’a na kasa, Muhammad Ali Pate, ya jaddada muhimmancin...

Labarai3 days ago

ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro

Kungiyar Tuntubar Arewa, wato Arewa Consultative Forum (ACF) ta ce a halin yanzu, batun da ya fi damun al’ummar arewacin...

Labarai3 days ago

Hukumar NOA Ta Yabawa Majalisar Jihar Nasarawa Wajen Samarda Dokoki Masu Amfani ga Jama’a

Hukumar Wayar da Kan Jama’a da Fadakarwa ta Kasa (NOA) ta yaba wa Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa bisa ga kafa...

Kasuwanci4 days ago

Shugaba Tinubu Ya Gana da Firayim Ministan Sin, Ya Ce Afirka Na Da Damar Zuba Jari da Haɓaka

  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ce Afrika na da manyan damammaki wajen zuba jari, ci gaba, da haɓaka tare...

Labarai4 days ago

Tinubu Ya Jajantawa Jihar Yobe Kan Rashe-Rashen Rayukan da Aka Yi a Tarmuwa

  Shugaba Bola Tinubu ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Yobe kan rashin rayukan da aka yi a Mafa a...

Mafi Shahara