Ilimi
Majalisar Wakilai Na Bukatar Sanin Dalilin Da Ke Sa Jirgin Kasan Abuja Kaduna Ke Goce Hanya
Majalisar Wakila zata gayyaci Ministan sufuri domin ya yima yan Najeriya bayanin abinda ya janyo jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja yake sauka daga kan laying dogo Wanda hakan Kan iya haifar da mummunan hadari ga rayuwar fasinjoji.
jirgin bukaci a gudanar da bincike kan musabbin abin da ke sa jirgin kasan Abuja- Kaduna ke karkacewa daga layin dogo wanda Kan iya haifar da mummunan hatsari ga rayuwar fasinja.
Hakan ya biyo bayan Kudurin gaggawa ne da Danmajalisa Mai wakilar mazabar Makarfi Kudan a Jihar Kaduna Alhaji Uamr Shehu Ajilo ya gabatar a zauren Majalisar da aka amince dashi.
Da yake gabatar da kudirin Alhaji Umar Shehu Ajilo ya koka ganin yadda Jirgin ke yawan turgudewa daga layin dogo inda hakan ka iya shafar sufirin jiragen kasa duk da irin gudunmawar da sashen ke bayarwa wajen tsaron lafiya da dukiliyar al’umma baki daya.
To amma yanda jirgin kasan Kaduna – Abuja yake yawan karkacewa daga hanyarsa na haifar da barzana ga rayuwar fasinjoji, lamarin ya Sanya bukatar mu hadakai domin daukar mataki.
Ya ce ganin yadda jirgin kasan yake jigilar fasinjoji da kaya da dama daga Kaduna zuwa Abuja, sannan yana bada gagarumar gudunmawa a fannin ci cigaban tattalin arziki da alummar Najeriya akwai bukatar majalisar ta sauki mataka gaggawa son gudun jefe al’umma cikin halin ni ‘yasu.
Alhaji Umar Ajilo, ya Kara da cewa abin takaici ne yadda jirgin kasan ke yawan sauka daga layin dogo, na baya bayan nan shi ne wanda ya faru a tashar jirgin kasa ta garin Asha da ke Babban birnin tarayya Abuja inda ya bar fasinjoji kara zube bayan Wanda ya faru a makonni biyu da suka gabata.
Ya cigaba da cewa wajibi ne Majalisar Wakilai ta gudanar da bincike domin gani dalilan da suka sa Jirgin kasan Kaduna-Abuja ne kadai yake fuskantar irin wannan Matsalar domin kare aukuwar lamarin anan gaba.
Da take amincewar da kudurin Majalisar ta umarci kwamitinta ya gayyaci ministan sufiri da sauran Jagororin a bangaren sufurin jiragen kasan da su zo su yi mata bayani don lalubo hanyoyin maganve sake faruwar hakan a nan gaba.
Ana sa ran Kwamitin ya gudanar da binciken sa cikin makonni hudu da gabatar da rahoton sa a zauren majalisar don daukan Madaki na gaba.
COV : TSIBIRI
-
Kasuwanci7 days ago
PDP Katsina Ta Zabi Sabbin Shugabanni
-
Labarai6 days ago
Kamfanin Mai Na Kasa Na Fuskantar Matsalolin Kudaden Samar Da Man Fetur
-
Labarai6 days ago
Gwamna Lawal Ya Yi Sabon Nadi Ga Hukumar Asusun Kula Da Harkokin Tsaro
-
Kasuwanci6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Rukunan Gidaje 500 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaba Bola Tinubu Ya Jajantawa Iyalan Yar’Adua Bisa Rasuwar Hajiya Dada
-
Labarai7 days ago
Ku Gaggauta Kammala Ayukkan Da Ke Hannun Ku A Arewa Maso Gabas
-
Labarai3 days ago
ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro
-
Labarai6 days ago
APC Ta Lashe Dukkan Kujerun Kansiloli Da Kansiloli A Kebbi