Kasuwanci
Gwamnan Niger Ya Kaddamar Da Shirin Kula da Lafiyar ‘Yan Fansho Da Tsofaffi
Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja ya kaddamar da kunshin inshorar lafiya, wani shiri da aka tsara don samar da muhimmin tallafi ga wadanda suka yi ritaya da tsofaffi a jihar.
Mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin yada labarai da dabarun zamani Abdullberqy Usman Ebbo a shafin sa na X, ya ce kaddamar da shirin a Minna na nuna gagarumin ci gaba a kokarin da jihar ke yi na kula da kiwon lafiya tare da jajircewa wajen kyautata rayuwar al’ummarta.
Abdullberqy Ebbo ya bayyana cewa an tsara shirin ne don kawar da matsalolin kudi ga harkar kiwon lafiya, da baiwa masu ritaya da tsofaffi damar samun muhimman ayyukan kiwon lafiya mai kyau a rayuwarsu.
A cewarsa cikakken kunshin ya kunshi jiyya, magunguna, da tuntubar juna tsakanin wata babbar hanyar sadarwa ta masu ba da lafiya a jihar Neja.
Mai ba da shawara na musamman kan kafafen sadarwa na zamani da dabarun zamani ya kara bayyana cewa babban sakataren hukumar kula da lafiya ta jihar Neja, Malam Sulayman Abu_Bakr ya jaddada kudirin gwamnatin na samar da tsarin kula da lafiya.
Sulayman Abu-Bakr ya kuma bayyana irin gudunmawar da dattawa ke bayarwa ga ci gaba don haka bukatar wadanda suka yi ritaya su ji daɗin shekarunsu na ƙarshe cikin mutunci da kuma samun damar samun muhimman ayyukan kiwon lafiya.
Abdulbaqy Ebbo ya kara da cewa, taron ya nuna kwazon da Gwamna Mohammed Umar Bago ya jagoranta wajen inganta rayuwar al’ummarta, musamman ma tsofaffi wanda ya nuna kyakkyawan mataki na samar da ingantaccen tsarin kiwon lafiya a jihar Neja.
ALIYU LAWAL/Wababe
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar