Connect with us

Labarai

Putin Ya Gargaɗi Koriya ta Kudu Game Da Bai Wa Ukraine Makamai

Published

on

Shugaban Vladimir Putin ya gargaɗi Koriya ta Kudu kan abin da ya kira “babban kuskure” idan ta sake ta aika wa Ukraine makamai a yaƙin da take yi da Rashar.

Kalaman nasa na zuwa ne bayan Seoul ta ce tana duba yiwuwar yin hakan a matsayin martani ga yarjejeniyar tsaro da Rashar ta ƙulla da Koriya ta Arewa domin taimaka wa juna idan wata ƙasa ta kai wa ɗayarsu hari.

Moscow “za ta…[ɗauki] matakin da ba lallai ya yi wa shugabannin Koriya ta Kudu daɗi ba idan ta bai wa Ukraine makamai”, kamar yadda Mista Putin ya shaida wa manema labarai ranar Alhamis.

Shugaban na Rasha na magana ne a Vietnam jim kaɗan bayan ziyarar da ya kai Pyongyang babban birnin Koriya ta Arewa, inda suka saka hannu kan yarjejeniyar tare da Shugaba Kim Jong Un.

Putin ya kuma yi gargaɗin cewa Rasha za ta bai wa Koriya ta Arewa makamai idan Amurka da ƙawayenta suka ci gaba da bai wa Ukraine makamai.

Waɗanda suke bayar da waɗannan makaman suna tunanin cewa ba yaƙi suke yi da mu ba. Na faɗa cewa baya ga Koriya ta Arewa, muna da ‘yancin tura makamai zuwa sassan duniya,” a cewar Putin.

Tun da farko Koriya ta Kudu ta yi tir da yarjejniyar da ƙasashen suka ƙulla a matsayin wata barazana ga tsaron ƙasarta, har ma mai ba da shawara kan tsaro Chang Ho-jin ya ce ƙasarsa na shirin “duba bai wa Ukraine makamai”.

Yayin da Koriya ta Kudu ta bai wa Ukraine tallafin kayayyaki da kuma was kayan aikin soji, zuwa yanzu ba ta ba ta makaman yaƙi ba sakamakon tsarinta na ƙin bai wa wata ƙasa makamai matuƙar tana cikin yaƙi.

Yayin ziyarar, Mista Kim ya bayyana “cikakken goyon bayansa” ga mamayar da Rasha ke yi wa Ukraine. Akwai hujjoji masu ƙwari da ke nuna tuni Rashar ta fara amfani da makaman Koriyar a kan

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Fasaha52 mins ago

MDD Ta Yi Alla-Wadai Da Harin Isra’ila Kan Wata Makaranta A Gaza

Hukumar kula da ƴan gudun hijirar Falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya (Unrwa), ta yi Alla-wadai da harin da Isra’ila ta...

Labarai1 hour ago

‘Sakamakon Da Ghana Ke Samu Abin Kunya Ne A Wurinmu’

Ghana na daf da rasa damar halartar gasar nahiyar Afrika karon farko tun shekarar 2004, kuma yanzu haka ana ta...

Fasaha1 hour ago

Gwamnatin Kano Za Ta Hada Hannu Da Tsofaffin Dalibai Domin Inganta Ilimi

Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta bayyana shirinta na hada kai da Tsofaffin Kungiyoyin dalibai a fadin Jihar domin inganta...

Kasuwanci1 hour ago

Jihar Neja Ta Kafa Hukumar Kayyade Farashin Kayyakin Masarufi

Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja ya amince da kafa hukumar kula da farashin kayyaki ta jihar Neja.  ...

Labarai2 hours ago

Tawagar Gwamnatin Tarayya Tayi Jaje Ga Al’ummar Jigawa

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya aike da tawaga domin jajantawa iyalan wadanda suka rasu a Majia, karamar hukumar Taura...

Kasuwanci2 hours ago

Dattawan Jam’iyar PDP Na Fadi Tashin Hade Kan ‘Ya’yan Jam’iyar – Abba Moro

Majalisar dattawan jam’iyyar PDP ta yi kira ga kungiyoyi masu fada a ji a jam’iyyar da su rungumi zaman lafiya...

Kasuwanci2 hours ago

Kano Ta Bada Miliyan 100 Ga Wadanda Fashewar Tankar Mai Ta Shafa A Jigawa

Gwamnatin jihar Kano ta bayar da tallafin naira miliyan dari ga wadanda fashewar tanka ta shafa a garin Majia da...

Ilimi2 hours ago

Babu Aljannu Ko Rauhanai A Batun Ciwon Kwakwalwa – Dr. Poul

Wani likitan dake aiki a asibitin koyarwa na jami’ar tarayya da ke lafiya, jihar Nasarawa Dr. Paul Agboand ya ce...

Kasuwanci2 hours ago

An Ƙaddamar Da Kwamitoci 6 Don Ƙara Inganta Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa ƙa’idojin gudanar da nagartattun ayyukan gwamnati a cikin ma’aikatun...

Fasaha2 hours ago

Dalibai Sun Babbake Gidan Shugaban Kwalejin Kimiyya A Birnin Kebbi

Daliban kwalejin kimiyya da fasaha ta Jega da ke jihar Kebbi sun kona gida da motar Shugaban kwalejin kimiyya da...

Mafi Shahara