Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Ginin Filin Jiragen Sama Na Gusau
Ministan Sufurin Jiragen Sama, Dr. Festus Keyamo, ya kaddamar da aikin gina filin jiragen sama na Gusau a jihar Zamfara, kan kudi naira biliyan sittin da biyu.
A lokacin da yake kaddamar da aikin, Ministan ya bayyana filin jiragen saman a matsayin abin alfahari ga jihar da ma kasa baki daya.
Ya bayyana cewa, aikin filin jirgin zai kara habbaka harkokin noma da kasuwanci na al’ummar jihar yana mai cewa, amfanin noma da kasuwanci a jihar ko shakka babu za su ci gaba da bunkasa filin jirgin.
Festus Kiyamo ya ci gaba da bayyana cewa, tuni tawagar kwararru ta fara aiki ba dare ba rana don ganin cewa aikin ya tabbata, ya kara da cewa, gwamnatin tarayya za ta ba da duk wani tallafi da gudummawar da ake bukata domin samun nasarar aikin.
A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya ce za a ba da kulawar da ta dace domin samun nasarar kammala filin jirgin cikin wa’adin da aka kayyade da yarjejeniyar kwangilar watanni 32.
Ya ce idan aka kammala aikin zai taimaka wajen samar da ayyukan yi da kuma rage radadin talauci, ba ma a jihar kadai ba har da kasa baki daya.
Sani Haruna Dutsinma
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai7 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai7 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai7 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai5 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai7 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar