Connect with us

Ilimi

Gwamnati Za Ta Yiwa Madatsar Ruwan Alau Garanbawul A Barno

Published

on

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na yin garambawul tare da tabbatar da madatsar ruwa ta Alau da ke Maiduguri a jihar Borno ba ta sake zama hadari ga al’umma ba.

 

Ministan albarkatun ruwa da tsaftar mahalli, Joseph Utsev ya ba da wannan tabbacin a lokacin da ya jagoranci kwamitin ma’aikatun kasar a ziyarar tantance madatsar ruwa.

 

Ziyarar ta kwamitin ta biyo bayan mummunar ambaliyar da aka yi a ranar 10 ga watan Satumba, wadda ta yi sanadin salwantar rayuka da dama, tare da raba sama da mutane miliyan guda, tare da lalata muhimman ababen more rayuwa da filayen noma na biliyoyin naira a sassan jihar.

 

Ministan wanda Daraktan madatsun ruwa a ma’aikatar, Malam Aliyu Dala ya wakilta, ya bayyana cewa, wurin da ya rufta, wanda ya kai ga ambaliya a Maiduguri da kewaye, shi ne babban abin da aka fi mayar da hankali wajen tantancewar.

 

Utsev ya jaddada cewa, kwamitin zai yi nazari kan yanayin da dam din ke ciki, da kuma tasirinsa na zamantakewa da muhalli ga al’ummomin yankin, inda ya kara da cewa, manufar ita ce samar da mafita na gajeren lokaci da na dogon lokaci don hana bala’o’i a nan gaba.

 

Ministan ya tabbatar da aniyar gwamnati na kammala ayyukan kwamitin kafin damina mai zuwa.

 

Shugaban kwamatin da ke kula da madatsar ruwan Alau na jihar Borno, Alhaji Mohammed Sanda ne ya jagoranci tawagar zagayen gine-ginen madatsar ruwan.

 

Ya kara da cewa mazauna Maiduguri sun dogara ne da ruwa daga madatsar ruwan domin amfanin yau da kullum, yana mai alakanta ambaliya da aka yi a baya-bayan nan da ruwan sama mai yawa, tare da toshe hanyoyin ruwa, da karkatar da ruwa zuwa tafkin Alau.

 

Kwamitin ma’aikatun ya hada da kwararru daga ma’aikatun albarkatun ruwa da tsaftar muhalli, ayyuka da gidaje, muhalli, kasafin kudi, da kuma wakilai daga ofishin mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasa, da kungiyar Injiniyoyi ta Najeriya (NSE), da kuma majalisar. Tsarin Injiniya a Najeriya (COREN).

 

Cov/Dauda/Wababe

Labarai

Ilimi20 hours ago

Gwamnati Za Ta Yiwa Madatsar Ruwan Alau Garanbawul A Barno

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na yin garambawul tare da tabbatar da madatsar ruwa ta Alau da ke Maiduguri a...

Fasaha20 hours ago

Majalisar Zartaswar Jihar Jigawa Ta Fitar Kudaden Tallafin Karatu

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da kudi sama da naira miliyan dari bakwai da casa’in da takwas domin...

Labarai21 hours ago

Kungiyar Tsoffin Manyan Sakatarorin Zamfara Ta Sami Kyautar Mota

Gwamna Lawal Ya Ba Da Kyautar Mota Ga Ƙungiyar Tsaffin Manyan Sakatarorin Da Suka Yi Ritaya A Zamfara Gwamnan Jihar...

Labarai21 hours ago

An Tsinci Gawar Tauraron Mawakan One Direction Liam Payne

Liam Payne, ɗaya daga cikin mawaƙa a tawagar One Direction, ya mutu a Argentina bayan ya faɗo daga hawa na...

Labarai21 hours ago

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Wadanda Fashear Tankar Mai Ta Shafa A Jigawa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayyana matukar alhininsa dangane da mummunan fashewar tankar da ta afku a garin Majiya...

Ilimi22 hours ago

Hukumar Hisbah Ta Ziyarci Majalisar Dokokin Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar tabbatar da ingantattun tsare-tsare na walwala ga ma’aikatan Hisba domin tabbatar...

Fasaha22 hours ago

Za A Fafata A Gasar Tseren Doki Ta Masarautar Gwandu

Ana sa ran al’ummomin duniya daga Hadaddiyar Daular Larabawa da kasashen yammacin Afirka za su halarci gasar tseren doki na...

Kasuwanci22 hours ago

Gwamnan Niger Ya Kaddamar Da Shirin Kula da Lafiyar ‘Yan Fansho Da Tsofaffi

Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja ya kaddamar da kunshin inshorar lafiya, wani shiri da aka tsara don samar...

Labarai22 hours ago

Kamala Harris Ta Yi Alkawarin Sauya Salon Mulkin Amurka Idan Ta Lashe Zabe

Ƴar takarar shugabancin Amurka a jam’iyyar Democrat, Kamala Harris, ta yi alƙawarin sauya salo daga irin kamun ludayin shugaba Joe...

Labarai4 days ago

Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa

Jam’iyyar PDP a Jihar Nasarawa ta ce ba za ta yi takara a zaben  kananan hukumomi da za a gudanar...

Mafi Shahara