Labarai
Shugaba Tinubu Ya Yi Watsi Da Kudirin Dokar Karin Wa’adin Ma’aikatan Majalisa
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi watsi da kudirin dokar tsawaita wa’adin ma’aikatan majalisa da ke neman kara shekarun ritayar ma’aikatan.
Matakin da shugaban ya dauka na kunshe ne a cikin wata wasika da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta a zauren majalisar a lokacin da ta koma zamanta na yau Talata.
Kudirin ya bukaci a kara shekarun ritayar ma’aikatan majalisar zuwa shekaru 65 ko kuma shekaru 40 na aiki.
Wannan ya sabawa dokar da ta tanadi shekaru sittin ko kuma shekaru talatin da biyar na ritayar ma’aikatan gwamnati.
Shugaba Tinubu bai bayar da wasu takamaiman dalilai na hana amincewa da kudirin ba wanda ya haifar da cece-kuce.
Tun a watan Fabrairu ne majalisar dattawa ta yi watsi da kudirin amma ta sake nazari tare da zartas da shi da kuma yin irinsa a majalisar wakilai.
Daga Bashir Meyere
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar