Connect with us

Labarai

Annobar Kolera Ta Kashe Mutum Fiye Da 400 A Sudan

Published

on

Fiye da mutum 430 ne suka mutu sakamakon annobar kolera a ‘ƴan watannin da suka gabata, a daidai lokacin da yaƙin basasar ƙasar ke ci gaba a ƙasar, in ji ma’aikatar lafiyar ƙasar.

Alƙaluman waɗanda suka kamu da cutar sun ƙaru zuwa kusan 14,000 kamar yadda ma’aikatar lafiyar ƙasar ta sanar.

Sanarwar ta ce gwamnati na yin duk abin d aya kamata wajen “daƙile annobar a jihohin da annobar ta ɓarke.”

Rikicin da ke wakana a Sudan ɗin na matuƙar shafar samar da magunguna ga waɗanda abin ya shafa. Rikicin dai ya yi sanadiyyar mutuwar mutum fiye da 150,000 tun bayan fara yaƙin a bara kamar yadda wakilin Amurka na musamman a Sudan, Tom Perriello ya sanar.

Likitocin ƙasa da ƙasa sun ce “suna samun matsala daga dukkannin ɓangarorin biyu masu yaƙi da juna, abin da ya sa ayyukan jinƙai suka gaza samun masu buƙata.”

Ministan Lafiyar ƙasar, Haitham Mohammed Ibrahim ya ayyana ɓarekewar kolerar ne a tsakiyar watan Agusta.

Baya ga yaƙin da ake yi, ruwan sama da ambaliya da suka janyo cunkoso a sansanoni sun taimaka wajen ɓarkewar cutar ta kolera,

Esperanza Santos, jagoran ƙungiyar likitocin ƙasa da ƙasa a Sudan ya ce “waɗannan abubuwa su ne suka haɗu suka haifar da annobar.

A wasu yankunan ma an umarci makarantu da kasuwanni da shaguna da su rufe domin daƙile yaɗuwar annobar.

 

BCC

Labarai

Ilimi20 hours ago

Gwamnati Za Ta Yiwa Madatsar Ruwan Alau Garanbawul A Barno

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na yin garambawul tare da tabbatar da madatsar ruwa ta Alau da ke Maiduguri a...

Fasaha20 hours ago

Majalisar Zartaswar Jihar Jigawa Ta Fitar Kudaden Tallafin Karatu

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da kudi sama da naira miliyan dari bakwai da casa’in da takwas domin...

Labarai21 hours ago

Kungiyar Tsoffin Manyan Sakatarorin Zamfara Ta Sami Kyautar Mota

Gwamna Lawal Ya Ba Da Kyautar Mota Ga Ƙungiyar Tsaffin Manyan Sakatarorin Da Suka Yi Ritaya A Zamfara Gwamnan Jihar...

Labarai21 hours ago

An Tsinci Gawar Tauraron Mawakan One Direction Liam Payne

Liam Payne, ɗaya daga cikin mawaƙa a tawagar One Direction, ya mutu a Argentina bayan ya faɗo daga hawa na...

Labarai21 hours ago

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Wadanda Fashear Tankar Mai Ta Shafa A Jigawa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayyana matukar alhininsa dangane da mummunan fashewar tankar da ta afku a garin Majiya...

Ilimi22 hours ago

Hukumar Hisbah Ta Ziyarci Majalisar Dokokin Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar tabbatar da ingantattun tsare-tsare na walwala ga ma’aikatan Hisba domin tabbatar...

Fasaha22 hours ago

Za A Fafata A Gasar Tseren Doki Ta Masarautar Gwandu

Ana sa ran al’ummomin duniya daga Hadaddiyar Daular Larabawa da kasashen yammacin Afirka za su halarci gasar tseren doki na...

Kasuwanci22 hours ago

Gwamnan Niger Ya Kaddamar Da Shirin Kula da Lafiyar ‘Yan Fansho Da Tsofaffi

Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja ya kaddamar da kunshin inshorar lafiya, wani shiri da aka tsara don samar...

Labarai22 hours ago

Kamala Harris Ta Yi Alkawarin Sauya Salon Mulkin Amurka Idan Ta Lashe Zabe

Ƴar takarar shugabancin Amurka a jam’iyyar Democrat, Kamala Harris, ta yi alƙawarin sauya salo daga irin kamun ludayin shugaba Joe...

Labarai4 days ago

Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa

Jam’iyyar PDP a Jihar Nasarawa ta ce ba za ta yi takara a zaben  kananan hukumomi da za a gudanar...

Mafi Shahara