Labarai
Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
Kungiyar Sanatocin Arewa ta yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa rattaba hannu kan kudirin hukumar raya yankin Arewa maso Yamma ta zama doka
Wasikar yabon wacce shugaban kungiyar Abdulaziz ‘Yar’adua ya sanya wa hannu, ta ce wannan gagarumar nasara da aka samu ta kara sanya kwarin gwiwa kan kudirin gwamnati na bunkasa al’umma musamman yankin Arewa maso Yamma.
Ya kara da cewa hangen nesa irin na Shugaba Tinubu ya karfafa gwiwar al’umma na inganta tsaro a shiyyar Arewa maso Yamma da ke fama da matsalar tsaro a ‘yan shekarun nan.
Abdulaziz ‘Yaradua ya kuma bayyana cewa kafa hukumar wani muhimmin mataki ne na magance matsalolin da suke haifar da rashin tsaro, da suka hada da talauci, da rashin aikin yi, da rashin samun damammaki da sauransu.
Shugaban kungiyar sanatocin ya kuma bayyana cewa, “mayar da hankali ga hukumar wajen magance matsalar karancin abinci da bunkasa noma, zai yi tasiri kai tsaye ga rayuwar al’ummar mu, wadanda suke fafutuka wajen samun kayayyakin masarufi“.
“Kokarin da gwamnatinka ke yi na farfado da fannin noma na tabbatar da samar da abinci, zai kuma samar da ayyukan yi da bunkasar tattalin arziki“.
Ya bayyana jin dadinsa da cewa hukumar za ta ba da fifiko wajen magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta a yankin, duba da yadda ilimi shi ne ginshikin ci gaba, kuma kudurin da shugaba Tinubu ya yi na ganin cewa dukkan yaran Nijeriya sun samu ilimi mai inganci abin a yaba ne.
“Haka kuma, farfado da sana’ar auduga a yankin Arewa, wadda a da ta kasance bangaren ci gaban tattalin arziki, zai yi matukar tasiri ga tattalin arziki, kuma tabbas za a iya samar da ayyukan yi, da samar da arziki, da bunkasar masana’antu“.
A wani labarin kuma mataimakin majalisar dattawa Barau Jibrin ya yabawa shugaban kasa Bola Tinubu bisa amincewa da kudirin kafa hukumar.
Mataimakin shugaban majalisar dattawan ya yi imanin cewa hukumar za ta taimaka wajen samar da ci gaba a fadin jihohi bakwai na shiyyar.
Ya kuma ba da tabbacin cewa masu ruwa da tsaki a shiyyar, za su hada kai don ganin hukumar ta ci gaba da aiki da manufar kafa ta, don haka ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su ci gaba da marawa shugaba Bola Tinubu baya domin cigaban kasa.
Bashir Meyere
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar