Ilimi
Mata Da Marasa Galihu Za Su Amfana Da Tallafin Naira Miliyan 110 A Jihar Kabi
Asusun kula da kananan Yara na Majalisar Dunkin Duniya UNICEF, ya shirya bada na Naira miliyan 110 ga matalauta dubu 10,200 domin ba su damar samun ayyukan kiwon lafiya kyauta a jihar Kebbi.
Shugaban ofishin UNICEF na Sokoto, Michael Juma, wanda ya bayyana hakan a wata ziyarar ban girma da ya kai wa Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kuma ba da tabbacin cewa UNICEF ta himmatu wajen taimaka wa matalauta da mata da yara marasa galihu domin samun ayyukan kiwon lafiya musamman mazauna karkara.
Yayin da yake nuna godiyar UNICEF ga Gwamna Idris da ya jagoranci gwamnatinsa kan aiwatar da wasu tsare-tsare na yara da mata don ci gaban jama’a baki daya, ya yaba wa Gwamnan bisa amincewa da aiwatar da wasu manufofi, dokoki, da tsare-tsare kan lokaci da za su tabbatar da ci gaban al’umma a jihar.
Hukumar ta amince da kafa kotuna guda biyu a cikin babban birnin jihar, Birnin Kebbi, wadanda za su gabatar da duk wasu shari’o’in da suka shafi take hakkin yara musamman cin zarafin mata da kuma bayar da tabbacin UNICEF na bayar da goyon baya wajen tabbatar da kotunan sun cika ka’idojin da aka shimfida na yara a duniya.
A nasa jawabin, Gwamna Nasir Idris, ya godewa UNICEF bisa kokarin da take yi wa al’ummar jihar ta hanyar aiwatar da shirye-shirye daban-daban da nufin inganta rayuwar mata da yara musamman a fannin kiwon lafiya, ilimi, abinci mai gina jiki, da manufofin zamantakewa.
Abdullahi Tukur/Wababe
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar