Fasaha
Majalisar Zartaswar Jihar Jigawa Ta Fitar Kudaden Tallafin Karatu
Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da kudi sama da naira miliyan dari bakwai da casa’in da takwas domin siyan kayayyakin abinci na agajin gaggawa na SEMA da kuma shirye-shiryen kayan agaji da shiga tsakani kamar yadda ma’aikatar ayyuka ta musamman ta gabatar.
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na Jihar Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron majalisar wanda Gwamna Umar Namadi ya jagoranta a gidan gwamnati dake Dutse.
A cewarsa, kayayyakin sun hada da buhunan masara da gero 6000, katon spaghetti 12,000 da kuma buhunan Garri 2000.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce a bisa kokarin da gwamnatin jihar ke yi na inganta harkar ilimi a jihar, majalisar ta amince da kashe sama da naira miliyan 740 domin bayar da kwangilar gina ajujuwa, dakunan gwaje-gwaje, bandakuna, dakunan gudanarwa, dakunan gwaje-gwaje na ICT. da kuma taron bita a wasu zababbun makarantu a fadin jihar.
Ya yi nuni da cewa makarantun sun hada da GDSTC Kafin Hausa da Babura, CGSSS- Roni & Jahun, GDSTC Gumel, Kanya Babba, GDSSS Ringim, Dutse da Hadejia.
Sagir ya ci gaba da bayyana cewa, majalisar ta kuma amince da biyan alawus alawus na kudi sama da naira miliyan 624 na sabbin dalibai 14,269 da aka tantance kuma suke karatu a jami’ar Sule Lamido kafin Hausa, da Kwalejin horasda Malamai ta Gumel, da Kwalejin kimiyya da fasaha ta jiha da ke Dutse da Hadejia da kuma Kwalejin Horasda malamai ta Hadejia da Kwalejin Nazarin Shari’a ta Ringim
USMAN MZ/Wababe
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar