Labarai
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya (IPMAN) ta nuna damuwarta bisa yiwuwar fuskantar matsalar karancin mai duk da karin farashin da aka samu.
Kungiyar ta ce an sami rashin matsaya tsakanin mambobin kungiyar da mahukuntan kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL).
Da yake zantawa da manema labarai a Ilorin, jami’in hulda da jama’a na IPMAN na kasa, Alhaji Okanlawon Olanrewaju, ya ce farashin da NNPC ke dorawa ‘yan kasuwa a halin yanzu ya yi yawa.
Kakakin na IPMAN, wanda ya bayyana cewa kamfanin na NNPCL ya nemi sayar wa ‘yan kasuwa mai a kan Naira dubu daya danaira 10 akan kowace lita, wanda hakan ya ma zarta yadda aka sayar da shi a gidajen mai na NNPCL din.
Ya bayyana cewa matsalar da IPMAN ke fuskanta a bangaren mai na da matukar daure kai, inda ya kara da cewa NNNPCL ne kadai ke karbar mai matatar Dangote.
Okanlawon, ya ce a halin yanzu mambobin IPMAN sun biya kusan Naira biliyan 15 a asusun NNPCL na tsawon watanni kuma ba su ba su man ba.
Mai magana da yawun kungiyar ta IPMAN ya ce ’yan kasuwar sun karbi bashin kudi a bankuna domin sayo man fetur, inda ya ce jinkirin biyan bashin na kara yawan kudin ruwa da za su biya.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar
-
Labarai4 days ago
Isra’ila Ta Lalata Wani Masallaci A Harin Lebanon