Fasaha
Za A Fafata A Gasar Tseren Doki Ta Masarautar Gwandu
Ana sa ran al’ummomin duniya daga Hadaddiyar Daular Larabawa da kasashen yammacin Afirka za su halarci gasar tseren doki na shekara-shekara na Masarautar Gwandu da za a yi a Birnin Kebbi, jihar Kebbi.
Da yake jawabi ga taron manema labarai Jami’in gudanarwar taron, Alhaji Mustapha Adamu Ka’oje da Sarkin Bargun Kaoje, ya ce Jamhuriyar Nijar, Jamhuriyar Benin, Senegal, Bokina Faso, Kamaru, Ghana da kuma Dubai ana sa ran za su fafata a gasar kofuna bakwai.
Ya ce taron na daga cikin gudunmawar da Masarautar ta bayar wajen baje kolin al’adun Masarautar Gwandu, da inganta hadin kai da fahimtar juna a tsakanin al’ummarta da kuma ba da damammaki ga dimbin matasanta da sauran ‘yan Nijeriya da sauran kasashen duniya su gani da sanin masu arzikin masarautar, al’adun gargajiya, musamman sana’o’in masarautu, wasanni da tufafi.
Ko’odinetan ya bayyana cewa, a tarihi Masarautar Gwandu ta yi suna a matsayin gidan wasan tseren dawaki da kuma cibiyar karramawar gargajiya inda ya ce taron ya kuma nemi samar da damammaki ga ‘yan kasuwa a jihar.
Adamu Ka’oje, ya bayyana cewa, bikin baje kolin noma zai ba da damammaki ga manoma da ’yan kasuwar don yin musayar ra’ayi tare da samun damar samar da kayayyaki da ayyuka iri-iri.
COV/Abdullahi Tukur/Wababe
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar