Labarai
Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Zamfara
Wasu da ake zargin ƴan bindiga sun toshe babbar hanyar Gusau zuwa Funtua mai cike da cunkoso tare da yin awon gaba da matafiya da dama.
Ƴan bindigar sun tare babbar hanyar da ke tsakanin al’ummar Kucheri da Magazu a karamar hukumar Tsafe, inda suka yi ta harbin kan mai uwa da wabi.
Mai magana da yawun ƴansandan jihar ta Zamfara, ASP Yazid Abubakar, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga gidan talabijin na Channels, ya ce an yi garkuwa da mutanen da ba a tantance adadinsu ba a harin.
Ya ce jami’an tsaro na can suna hoɓɓasa don ganin an ceto mutanen da aka tafi da su.
“Lamarin ya faru ne da yammacin jiya Asabar. Ƴan bindigar sun tare hanya suka fara harbin kan masu tafiya inda suka yi garkuwa da wasu daga cikinsu,” inji kakakin ƴansandan.
Ya ce jami’ansu tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro suna aiki tare don ganin an ceto waɗanda aka sace.
Sai dai Abubakar ya musanta rahotannin da ke cewa an yi garkuwa da ‘yansanda biyar a lokacin da suke artabu da ‘yan bindigar.
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar