Connect with us

Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Masu Shirin Zanga-Zanga Gargadi

Published

on

Rundunar Tsaron Najeriya ta gargadi masu shirin zanga-zangar yaki da tsadar rayuwa a Najeriya ta ce sojoji ba za su kyale su su tayar da fitina ba.

Hedikwatar Tsaron ta yi gargadin cewa sojoji ba za su zura ido ga a yi kone-kone da dangoginsu na karya doka da oda da sunan zanga-zangar ba.

Dubban ’yan Najeriya musamman matasa sun ayyana 1 ga watan Agusta da ke a matsayin ranar fara zanga-zangar gama gari ta tsawon kwanaki 10 a fadin kasar kan tsadar rayuwa da ta addabe su.

Masu zanga-zangar, mai taken kawo karshe mummunan shugabanci  — #EndBadGovernace — sun nuna damuwarsa kan tsananin yunwa da hauhawan farashin kayan masarufi fiye da kima da ake ci gaba da fama da su a kasar.

Amma da yake jawabi a Abuja ranar Alhamis, Daraktan yada labaran Hedikwatar Tsaron, Manjo-Janar Edward Buba, ya ce sojoji ba za su zuba ido Najeriya ta fada a cikin yanayin rashin doka da oda ba.

Manjo-Janar Edward Buba ya ce sojoji sun bankado shirin wasu miyagu na amfani da zanga-zangar domin kawo tashin hankali ta hanyar kai hare-hare kan dukiyoyin al’umma.

“Duk da cewa yan kasa na da yancin su gudanar da zanga-zangar lumana, amma ba su da yancin haddas karya doka ad kuma ta’addanci.”

“Abu mai sauki ne a fahimci cewa zanga-zangar da ke tafe za ta bi sahun wadda ake gudanarwa ce a kasar Kenya, wadda ita ma ta tashin hankali ce, kuma har yanzu ba a shawo kanta ba.”

Buba ya kara da cewa, “Soji ba za su nade hannu suka kasa ta koma babu bin doka da oda ba.

“Dalili kuwa shi ne mun ga irin illa da barnar da rashin bin doka suka yi a kasashen da muka gudanar da ayyukan wanzar da zaman lafiya, muamman a lokacin rundunar ECOMOG  ta kungiyar kasashen ECOWAS.”

Labarai

Ilimi18 hours ago

Gwamnati Za Ta Yiwa Madatsar Ruwan Alau Garanbawul A Barno

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na yin garambawul tare da tabbatar da madatsar ruwa ta Alau da ke Maiduguri a...

Fasaha19 hours ago

Majalisar Zartaswar Jihar Jigawa Ta Fitar Kudaden Tallafin Karatu

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da kudi sama da naira miliyan dari bakwai da casa’in da takwas domin...

Labarai19 hours ago

Kungiyar Tsoffin Manyan Sakatarorin Zamfara Ta Sami Kyautar Mota

Gwamna Lawal Ya Ba Da Kyautar Mota Ga Ƙungiyar Tsaffin Manyan Sakatarorin Da Suka Yi Ritaya A Zamfara Gwamnan Jihar...

Labarai20 hours ago

An Tsinci Gawar Tauraron Mawakan One Direction Liam Payne

Liam Payne, ɗaya daga cikin mawaƙa a tawagar One Direction, ya mutu a Argentina bayan ya faɗo daga hawa na...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Wadanda Fashear Tankar Mai Ta Shafa A Jigawa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayyana matukar alhininsa dangane da mummunan fashewar tankar da ta afku a garin Majiya...

Ilimi20 hours ago

Hukumar Hisbah Ta Ziyarci Majalisar Dokokin Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar tabbatar da ingantattun tsare-tsare na walwala ga ma’aikatan Hisba domin tabbatar...

Fasaha20 hours ago

Za A Fafata A Gasar Tseren Doki Ta Masarautar Gwandu

Ana sa ran al’ummomin duniya daga Hadaddiyar Daular Larabawa da kasashen yammacin Afirka za su halarci gasar tseren doki na...

Kasuwanci21 hours ago

Gwamnan Niger Ya Kaddamar Da Shirin Kula da Lafiyar ‘Yan Fansho Da Tsofaffi

Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja ya kaddamar da kunshin inshorar lafiya, wani shiri da aka tsara don samar...

Labarai21 hours ago

Kamala Harris Ta Yi Alkawarin Sauya Salon Mulkin Amurka Idan Ta Lashe Zabe

Ƴar takarar shugabancin Amurka a jam’iyyar Democrat, Kamala Harris, ta yi alƙawarin sauya salo daga irin kamun ludayin shugaba Joe...

Labarai4 days ago

Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa

Jam’iyyar PDP a Jihar Nasarawa ta ce ba za ta yi takara a zaben  kananan hukumomi da za a gudanar...

Mafi Shahara