Labarai
Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
Shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan kudirin doka don hanzarta samar da ci gaba a shiyyoyin kasar nan.
Shugaban kasan ya amince da kudurin dokar hukumar raya yankin Arewa maso Yamma na shekarar 2024, da kuma kudurin hukumar raya Kudu maso Gabas na shekara 2023.
Za a kafa hukumar raya yankin Arewa maso yamma ne domin saukaka sake gina tituna, gidaje, da wuraren kasuwanci da rikice-rikice da dama suka lalata, tare da magance talauci, rashin neman ilimi, matsalolin da suka shafi muhalli, da duk wani abu da ke haifar da kalubalen ci gaba a jihohin yankin Arewa maso yamma.
Bugu da kari, ita ma hukumar raya shiyyar Kudu maso Gabas an kafa ta ne domin tabbatar da sake ginawa da gyara tituna, gidaje, da sauran barnar da shiyyar ta fuskanta, tare da magance matsalolin muhalli, da sauran matsalolin da ke kawo cikas ga ci gaba a jihohin Kudu maso Gabas.
Shugaba Tinubu ya yi amanna da gina al’umma bisa cikakken adalci, daidaito da kuma hadin kai; don haka ya himmatu wajen tabbatar da samar da ci gaba mai inganci, da gudanar da mulki tare da samar da ingantattun ayyuka ga daukacin ‘yan Najeriya
Daga Bello Wakili
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar