Connect with us

Ilimi

Sau 8 Aka Aura Min ’Yan Boko Haram —Ɗalibar Chibok Mai Juna-Biyu

Published

on

Ɗaya daga cikin ’yan matan Chibok da aka sace a watan Afrilun 2014, mai suna Ihyi Abdul, a Jihar Borno, ta ce an tilasta mata auren maza takwas yayin da ta ke hannun Boko Haram.

Wakilinmu ya ruwaito yadda Rundunar Operation Haɗin Kai ta miƙa yarinyar Chibok da aka ceto tare da wasu mutum 332 ga gwamnatin Jihar Borno.
Mutum 332, ciki har da mata 110 da yara 220, an ceto su ne a yankin Bama-Pulka yayin wani samame da dakarun soji suka kai dajin Sambisa.
A yayin wani taron a sansanin Maimalari da ke Maiduguri, Manjo Janar Waheed Shuaibu, Kwamandan Operation Haɗin Kai, ya ce an ceto Ehi Abdul mai shekara 27, wacce ke ɗauke da juna biyu na wata uku, a ranar Talata tare da ’ya’yanta biyu a dajin Sambisa.

Da ta ke jawabi ga manema labarai a hedikwatar Operation Haɗin Kai a Maiduguri, ta ce, “Na yi tafiyar tsawon kwanaki kafin na isa wani wajen da sojojin Najeriya suke, inda suka karɓe ni da ’ya’yana.

“Na auri maza takwas kuma na haifi yara uku. Ban yi ƙoƙarin tserewa ba a baya saboda ban shirya tserewa ba sai a yanzu.

“Ba a ajiye ‘yan matan Chibok a sansani ɗaya, kuma ban san dalilin da ya sa ake tsare wasu tsare ba. Wasu daga cikinmu sun zaɓi zama a Sambisa, yayin da wasu ba su samu damar tserewa ba.

“Game da ilimi, ba zan iya cewa komai ba a yanzu, amma ba ni da tabbacin cewar zan iya ci gaba da karatu ba.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai1 day ago

Ziyarar Shugaba Tinubu Zuwa China Ta Yi Nasara

  Ziyarar Shugaba Tinubu zuwa China Ta Yi Nasara, da kuma Shaida Wa ‘Yan Najeriya Mazauna China, Yi Alkawarin don...

Labarai1 day ago

Sabon Tsarin Albashi: Majalisar Kano Ta Amince da Karin Kasafin Naira Biliyan 99

Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙarin kasafin kudi na N99bn da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Musanta Jita-Jitar Bayar Da Kudi Ga ‘Yan Ta’adda

  Gwamnatin Jihar Zamfara tayi watsi da jita-jitar da ke yawo cewar tana shirin bayar da kudi ga wasu sanannun...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Dauki Matakan Gaggawa Don Wadata Man Fetur da Farashinsa

  Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Ɗauki Matakai Masu Ƙarfi don Magance Samuwar Man Fetur da Farashi a Faɗin Najeriya A...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nemi Hadin Gwiwar Afirka da China Don Bunkasa Tattalin Arziki

  Shugaba Bola Tinubu ya yi kira da a ci gaba da hadin kai tsakanin Afrika da Sin, yana mai...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya ta Amince da Tsare-tsare Don Yakar Rashin Abinci Mai Gina Jiki

  Daga: Bello Wakili Ministan Tsare-tsare na Lafiya da Walwala ta Jama’a na kasa, Muhammad Ali Pate, ya jaddada muhimmancin...

Labarai3 days ago

ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro

Kungiyar Tuntubar Arewa, wato Arewa Consultative Forum (ACF) ta ce a halin yanzu, batun da ya fi damun al’ummar arewacin...

Labarai3 days ago

Hukumar NOA Ta Yabawa Majalisar Jihar Nasarawa Wajen Samarda Dokoki Masu Amfani ga Jama’a

Hukumar Wayar da Kan Jama’a da Fadakarwa ta Kasa (NOA) ta yaba wa Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa bisa ga kafa...

Kasuwanci3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Gana da Firayim Ministan Sin, Ya Ce Afirka Na Da Damar Zuba Jari da Haɓaka

  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ce Afrika na da manyan damammaki wajen zuba jari, ci gaba, da haɓaka tare...

Labarai3 days ago

Tinubu Ya Jajantawa Jihar Yobe Kan Rashe-Rashen Rayukan da Aka Yi a Tarmuwa

  Shugaba Bola Tinubu ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Yobe kan rashin rayukan da aka yi a Mafa a...

Mafi Shahara